fidelitybank

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Date:

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama mutum 398 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban a cikin wata babbar samame da aka ƙaddamar domin kawar da masu aikata laifi a fadin jihar.

Wannan farmaki da aka gudanar cikin kwanaki tara na farko, na ƙarƙashin wani rundunar haɗin gwiwa ta musamman da gwamnatin jihar ta kafa, inda rundunar ‘yan sanda ce jagora

Kakakin rundunar, DSP Mansir Hassan, ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar 18 ga Yuni, inda ya ce samamen ya biyo bayan sahihan bayanan sirri da suka kai ga ckama waɗanda ake zargi a wurare daban-daban na jihar.

Cikin wadanda aka kama har da wani sanannen jagoran ‘yan daba mai suna Mathew Adamu wanda aka ƙwace bindiga a tare da shi.

Haka kuma an kama wani shahararren mai safarar miyagun ƙwayoyi, Adamu Umar, wanda za a miƙa shi ga hukumar NDLEA domin ci gaba da bincike da gurfanarwa.

Rundunar ta kuma yi nasarar ƙwato wasu makamai masu haɗari da miyagun ƙwayoyi da kuma wayoyin salula guda 29 da aka sace a samamen

Kwamishinan ‘Yan Sandan jihar, CP Rabiu Muhammad, ya umarci rundunar ta musamman su ci gaba da zage damtse.

taraba state today news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An Kama wakilin jam’iyya da Naira miliyan 25.9 na Siyan Kuri’a

Jami’an tsaro sun kama wani da ake zargin wakilin...

Farashin kayan abinci na rugu-rugu a Najeriya – NBS

Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS) ta ce hauhawar farashin...

Kotun Kano ta ce a kamo mata Dagacin Tamburawa

Kotun Shari’ar Musulunci da ke shelkwatar Hisbah a Kano,...

Kotu ta ƙwace motocin gwamnatin Zamfara guda 40 daga hannun Matawalle

Kotun Daukaka Kara da ke a Sokoto ta tabbatar...

A na cigaba da gudanar da zaben cike gurbi harda Kano

Kano na ɗaya daga cikin jhihohin da ake kaɗa...

Mutane 12 sun mutu a wani hatsari a Kano – FRSC

Hukumar Kiyaye Haddura ta Ƙasa (FRSC) reshen Kano, ta...

Masarutar Rano ta haramta aurar da Yaran da ba su kammala karatun Firamare ba

Masarautar Rano a Kano ta haramta cire yarinya daga...

Matatar Dangote za ta fara jigilar mai kyauta ga gidajen mai

Matatar man Dangote za ta fara jigilar mai kyauta...

An sassata rikicin da aka shafe shekaru 30 kan Masallacin Sharada da Islamiyya

Tsohon dan takarar gwamnan Kano, Malam Sha’aban Ibrahim Sharada,...

Duk da kalubalen ‘yan siyasa a Kano mun shirya a zaben cike gurbi – INEC

Kwamishinan hukumar zaɓe mai zaman kanta (INEC) reshen jihar...

Barau ya jagorancin gangamin zaben cike gurbi a Kano

Barau ya samu rakiyar Karamin Ministan Gidaje da Raya...

Gwamnatin Kano ta kara fadada shirin matasa 

Gwamna Abba Kabir Yusuf na Jihar Kano ya sake,...
X whatsapp