Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama mutum 398 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban a cikin wata babbar samame da aka ƙaddamar domin kawar da masu aikata laifi a fadin jihar.
Wannan farmaki da aka gudanar cikin kwanaki tara na farko, na ƙarƙashin wani rundunar haɗin gwiwa ta musamman da gwamnatin jihar ta kafa, inda rundunar ‘yan sanda ce jagora
Kakakin rundunar, DSP Mansir Hassan, ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar 18 ga Yuni, inda ya ce samamen ya biyo bayan sahihan bayanan sirri da suka kai ga ckama waɗanda ake zargi a wurare daban-daban na jihar.
Cikin wadanda aka kama har da wani sanannen jagoran ‘yan daba mai suna Mathew Adamu wanda aka ƙwace bindiga a tare da shi.
Haka kuma an kama wani shahararren mai safarar miyagun ƙwayoyi, Adamu Umar, wanda za a miƙa shi ga hukumar NDLEA domin ci gaba da bincike da gurfanarwa.
Rundunar ta kuma yi nasarar ƙwato wasu makamai masu haɗari da miyagun ƙwayoyi da kuma wayoyin salula guda 29 da aka sace a samamen
Kwamishinan ‘Yan Sandan jihar, CP Rabiu Muhammad, ya umarci rundunar ta musamman su ci gaba da zage damtse.