fidelitybank

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Date:

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama mutum 398 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban a cikin wata babbar samame da aka ƙaddamar domin kawar da masu aikata laifi a fadin jihar.

Wannan farmaki da aka gudanar cikin kwanaki tara na farko, na ƙarƙashin wani rundunar haɗin gwiwa ta musamman da gwamnatin jihar ta kafa, inda rundunar ‘yan sanda ce jagora

Kakakin rundunar, DSP Mansir Hassan, ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar 18 ga Yuni, inda ya ce samamen ya biyo bayan sahihan bayanan sirri da suka kai ga ckama waɗanda ake zargi a wurare daban-daban na jihar.

Cikin wadanda aka kama har da wani sanannen jagoran ‘yan daba mai suna Mathew Adamu wanda aka ƙwace bindiga a tare da shi.

Haka kuma an kama wani shahararren mai safarar miyagun ƙwayoyi, Adamu Umar, wanda za a miƙa shi ga hukumar NDLEA domin ci gaba da bincike da gurfanarwa.

Rundunar ta kuma yi nasarar ƙwato wasu makamai masu haɗari da miyagun ƙwayoyi da kuma wayoyin salula guda 29 da aka sace a samamen

Kwamishinan ‘Yan Sandan jihar, CP Rabiu Muhammad, ya umarci rundunar ta musamman su ci gaba da zage damtse.

legitnewsnigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mutane 12 sun mutu a wani hatsari a Kano – FRSC

Hukumar Kiyaye Haddura ta Ƙasa (FRSC) reshen Kano, ta...

Masarutar Rano ta haramta aurar da Yaran da ba su kammala karatun Firamare ba

Masarautar Rano a Kano ta haramta cire yarinya daga...

Matatar Dangote za ta fara jigilar mai kyauta ga gidajen mai

Matatar man Dangote za ta fara jigilar mai kyauta...

An sassata rikicin da aka shafe shekaru 30 kan Masallacin Sharada da Islamiyya

Tsohon dan takarar gwamnan Kano, Malam Sha’aban Ibrahim Sharada,...

Duk da kalubalen ‘yan siyasa a Kano mun shirya a zaben cike gurbi – INEC

Kwamishinan hukumar zaɓe mai zaman kanta (INEC) reshen jihar...

Barau ya jagorancin gangamin zaben cike gurbi a Kano

Barau ya samu rakiyar Karamin Ministan Gidaje da Raya...

Gwamnatin Kano ta kara fadada shirin matasa 

Gwamna Abba Kabir Yusuf na Jihar Kano ya sake,...

An kaiwa Malamin addini hari a Kano bayan an jikatasu da Matarsa

Wani malamin addinin Musulunci, Malam Kabir Idris, da matarsa...

Kotun Kano ta daure wata Mata da ake zargin ta tsafe su

Kotun Majistiri mai lamba 7 da ke Nomansland, ƙarƙashin...

Dalibi ya kashe kansa a cikin Jami’a

Hukumar jami'ar Obafemi Awolowo da ke jihar Osun, sun...

Gobara na cigaba da lakume wasu yankunan Turai

Gobarar daji na ci gaba da ruruwa a sassan...

An kama Fursunoni 7 da suka tsere daga gidan kurkukun jihar Nasarawa

Hukumar kula da gidajen yari a Najeriya ta ce...
X whatsapp