fidelitybank

Bayan ɓacewar Tinubu na mako mako guda yanzu ya dawo Najeriya

Date:

A ranar Juma’a ne shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, ya dawo Najeriya bayan halartar taron Majalisar Dinkin Duniya karo na 78 da aka kammala a makon jiya.

A cikin makon da ya gabata, Ajuri Ngelale, mashawarcin shugaban kasa na musamman kan harkokin yada labarai, ya yi shiru kan inda Tinubu yake, wanda rahotanni suka ce ya bar birnin New York a ranar 22 ga watan Satumba.

Kusan mako guda ba a san inda Tinubu yake ba, har sai da ya dawo Najeriya a daren Juma’a, duk da cewa wasu rahotanni da ba a tabbatar ba sun ce ya taso ne daga birnin New York zuwa birnin Paris.

A taron UNGA da aka kammala kwanan nan, shugaban Najeriyar ya yi jawabi a zauren taron inda ya yi kira ga shugabannin kasashen duniya da su hada kai da kasashen Afirka wajen tunkarar kalubalen da suke fuskanta.

Tinubu, a matsayinsa na shugaban kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika, ECOWAS, ya nemi taimako domin sake kafa mulkin dimokuradiyya ta hanyar da za ta magance kalubalen siyasa da tattalin arziki da kasar ke fuskanta, ciki har da masu tsattsauran ra’ayi da ke neman haddasa rashin zaman lafiya a yankin.

A kan haka, shugaban ya kuma gana da masu zuba jari a Amurka kan bukatar bunkasa zuba jari a Najeriya.

Ya gana da ‘yan Najeriya a Amurka, inda ya bukace su da su zama jakadu nagari a kasar.

natforce latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp