fidelitybank

Bayan ɓacewar Tinubu na mako mako guda yanzu ya dawo Najeriya

Date:

A ranar Juma’a ne shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, ya dawo Najeriya bayan halartar taron Majalisar Dinkin Duniya karo na 78 da aka kammala a makon jiya.

A cikin makon da ya gabata, Ajuri Ngelale, mashawarcin shugaban kasa na musamman kan harkokin yada labarai, ya yi shiru kan inda Tinubu yake, wanda rahotanni suka ce ya bar birnin New York a ranar 22 ga watan Satumba.

Kusan mako guda ba a san inda Tinubu yake ba, har sai da ya dawo Najeriya a daren Juma’a, duk da cewa wasu rahotanni da ba a tabbatar ba sun ce ya taso ne daga birnin New York zuwa birnin Paris.

A taron UNGA da aka kammala kwanan nan, shugaban Najeriyar ya yi jawabi a zauren taron inda ya yi kira ga shugabannin kasashen duniya da su hada kai da kasashen Afirka wajen tunkarar kalubalen da suke fuskanta.

Tinubu, a matsayinsa na shugaban kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika, ECOWAS, ya nemi taimako domin sake kafa mulkin dimokuradiyya ta hanyar da za ta magance kalubalen siyasa da tattalin arziki da kasar ke fuskanta, ciki har da masu tsattsauran ra’ayi da ke neman haddasa rashin zaman lafiya a yankin.

A kan haka, shugaban ya kuma gana da masu zuba jari a Amurka kan bukatar bunkasa zuba jari a Najeriya.

Ya gana da ‘yan Najeriya a Amurka, inda ya bukace su da su zama jakadu nagari a kasar.

nigerian news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp