fidelitybank

Bawa ka sauka daga kujerar EFCC – Ƙungiyar Arewa

Date:

Gamayyar kungiyoyin farar hula a arewacin kasar nan, sun yi kira ga shugaban hukumar EFCC, Abdulrasheed Bawa, da ya yi murabus ko kuma a kore shi bisa zargin cin hanci da rashawa.

A wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi, shugaban gamayyar kungiyoyin farar hula na Arewa, Adamu Aminu Musa, ya bayyana cewa murabus din Abdulrasheed Bawa a wannan lokaci abu ne mai tsafta domin ceto martabar Najeriya.

Sanarwar ta ce: “Shugaban zartarwa na hudu, Mista Bawa, ya kasance kan gaba wajen zarge-zargen cin hanci da rashawa tun ma kafin a nada shi a matsayin shugaban, wanda aka yi imanin cewa yana tattare da cece-kuce da rufa-rufa.

Sanarwar ta kara da cewa Bawa yana aiki ne kamar sarki, inda yake amfani da ofishinsa wajen tursasasa, muzgunawa, da kuma tilastawa mutane yin abin da ya nema, ciki har da bankuna, wasu hukumomin gwamnati, da ‘yan Najeriya da ba su da wani laifi, tare da goyon bayan ubangidansa, babban lauyan gwamnati.

Adamu Aminu ya kuma yi zargin cewa Bawa ya tilastawa shugaban NIMASA daukar nauyin ‘yan uwansa zuwa kasashen waje karatu a jami’ar Centurion of Technology and Management, Bhubaneswar, India.

Ya yi zargin cewa shugaban na EFCC ya tursasa hukumar ta NCC tare da tursasa wa kaninsa aiki yayin da shi da kansa ya dauki wani dan gidan sa aiki a ofishin EFCC na Legas.

www.nigerianews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp