fidelitybank

Baturen ‘yan sanda a Jigawa ya rasu a ofishin sa

Date:

Baturan ‘yan sanda reshen karamar hukumar Jahun a jihar Jigawa, SP Abubakar Musa, ya fadi ya mutu a ofishin sa.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, DSP. Lawan Shiisu Adamu ya tabbatar da rasuwar a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a ranar Asabar.

Ya ce lamarin ya faru ne a ranar Juma’a da daddare da misalin karfe 9:00 na dare a ofishin DPO na sashen Jahun bayan doguwar jinya.

A cewarsa, “SP. Abubakar Musa ya rasu jiya da misalin karfe 9:00 na dare a lokacin da yake rufe bakin aikinsa.”

Ya bayyana cewa an garzaya da marigayin zuwa babban asibitin Jahun da kuma babban asibitin Rashid Shekoni sannan aka kai shi asibitin koyarwa na Aminu Kano inda aka tabbatar da rasuwarsa.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP. Emmanuel Ekot Effiom ya jajantawa iyalan mamacin da rundunar ‘yan sandan Najeriya.

www.najnew

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...
X whatsapp