fidelitybank

Batun Tinubu ya yi murabus karkatar da hankalin al’umma ne kawai – Mohammed Idris

Date:

Ministan yaɗa labarai da wayar da kai, Mohammed Idris, ya yi watsi da kiraye-kirayen da ake na shugaba Bola Tinubu ya yi murabus, inda ya ce yunƙuri ne na karkatar da hankalin mutane.

A makon da ya gabata ne wasu gwamnoni daga jam’iyyar PDP, babbar jam’iyyar adawa a Najeriya suka buƙaci shugaba Tinubu ya ajiye muƙaminsa idan ba zai iya warware ƙalubalen tattalin arzikin da ƙasar ke fama da shi ba.

A ranar Lahadi ne, Idris ya ce shugaba Tinubu ba zai ajiye aiki ba kuma yana da ƙwarewar magance taɓarɓarewar tattalin arziki.

Cikin wata sanarwa, ministan ya ce matsalolin tattalin arzikin da Najeriya ke fuskanta ba su fi ƙarfin shugaba Tinubu ba kuma ba zai ajiye muƙaminsa ba.

“Zai ci gaba da dagewa wajen yaƙar matsalolin har a samu galaba a kan su, shimfiɗa tubalin sabuwar Najeriyar da ke tasowa.”

Najeriya dai na fama da taɓarɓarewar tattalin arziki mafi muni cikin shekaru, inda darajar kuɗin ƙasar ke ƙara faɗuwa kuma jama’a da dama na fama wajen samun abin kai wa bakin salati.

vanguard newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp