Kungiyar makaman jami’o’i ta kasa ASUU ta sanar da tsunduma yajin aiki, bayan da kungiyar ta zauna zaman tattaunawa kan samar da masalaha.
Ya zuwa yanzu, gwamnati ta gagara cika alkawuran da ta dauka tsakaninta da ASUU, lamarin da bai yi wa kungiyar dadi ba.
Kungiyar ta sanar da dalibai da iyaye da daukacin al’umma abin da ke tsakaninta da gwamnatin Najeriya.
Punch ta rawaito cewa, a wani taron manema labarai da shugaban kungiyar, Farfesa Emmanuel Osodeke ya hada, inda ya yi jawabi kan batun a ranar Litinin 14 ga watan Fabrairu.
Osodeke ya bayyana cewa, a ranakun 13 da 14 ga watan Nuwamba, Shugaban ASUU, ya koka da cewa duk da ganawar da ya yi da Ministan Kwadago da Aiki, Dr. Chris Ngige, a ranar 14 ga Oktoba, 2021, kan batutuwan da kungiyar ke bore akai, gwamnati ta yi shuru. Bayan wannan barazanar, karamin ministan ilimi, Emeka Nwajiuba, ya yi alkawarin cewa za a biyawa kungiyar bukatunta. Makonni kadan, ASUU ta dakatar da yajin aikin da ta shirya yi, domin an biya malaman jami’o’in tarayya alawus na Naira biliyan 22.1. Shugaba Buhari ya gana da shugabanni, ciki har da na addinai kan lamarin da ya shafi yarjejeniyar gwamnati da ASUU ta 2009.