Ma’aikatar kudin Najeriya ta yi watsi da labaran cewa, shelkwatarta dake birnin tarayya Abuja ya kama da wuta da safiyar Laraba, 23 ga watan Febrairu, 2022.
Yunusa Tanko Abdullahi, mai magana da yawun Ministar kudi, Zainab Ahmed Shamsuna, ya bayyana haka a jawabin da ya wallafa a shafin hukumar na Facebook.
Tanko Abdullahi ya ce wani Batir ne kawai ya kama da wuta kuma da wuri a ka kashe wutar.