fidelitybank

Bashir Ahmad ya yi tsokaci kan gwamnan jihar Kano na gaba

Date:

Mataimaki na musamman ga shugaban kasa Muhammadu Buhari kan harkokin sadarwa na zamani, Bashir Ahmad, ya yi tsokaci kan gwamnan jihar Kano na gaba.

Ahmad ya bayyana cewa mataimakin gwamnan jihar a halin yanzu, Nasiru Gawuna yana da kwarewar jagorantar jihar Kano.

Ya yi nuni da cewa Gawuna na da ikon yin tasiri mai kyau kuma mai dorewa ga al’ummar jihar.

Karanta Wannan: Ba zan amince da tayin Tinubu ba – Peter Obi

A wani sako da ya wallafa a shafinsa na twitter, mai taimaka wa shugaban kasar ya bayyana Gawuna a matsayin kwararre mai kula da harkokin gudanarwa.

Ya rubuta: “Babu shakka Nasiru Gawuna kwararre ne mai gudanar da mulki, wanda ya kware a aikin gwamnati da kuma fahimtar kalubalen da Kano ke fuskanta a yau.

“Ina da cikakken kwarin gwiwa kan iyawar Dokta Gawuna na jagorantar Jihar mu zuwa ga kyakkyawar makoma.

“A matsayinsa na Gwamna zai yi tasiri mai dorewa a rayuwar Kanawa.”

vanguard news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp