Tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo, ya bayyana karuwar basussukan Najeriya a matsayin wata babbar matsala ga al’ummar yanzu da masu zuwa.
Obasanjo ya bayyana hakan ne yayin wani shiri mai taken “Boiling Point Arena”.
Bashin Najeriya ya haura Naira Tiriliyan 12.6 a cikin watanni uku, inda ya kai N134.3 tiriliyan ($91.3bn) a karshen kwata na biyu na shekarar 2024.
Wannan ya nuna karuwar kashi 10.35 cikin 100 daga Naira tiriliyan 121.7 da aka samu a rubu’in farko na shekarar.
Da yake mayar da martani, Obasanjo ya ce, “Eh, na sami damar yafewa al’ummar kasa basussuka kafin in bar mulki, amma yanayin bashin da muke bi yanzu matsala ce ga wannan da na gaba.”
Obasanjo ya buga misali da kasashen Koriya ta Kudu da Singapore a matsayin misali na kasashen da ci gaban da suka samu ya samo asali ne daga shugabanci na gaskiya da rikon amana.
A cewarsa, hanya mafi dacewa ta yaki da cin hanci da rashawa ita ce daga sama.
“Hanya mafi kyawun yaki da cin hanci da rashawa daga sama. A Koriya ta Kudu, shugabanninsu na yin nade-nade bisa cancanta, kuma hakan ya zama gadon kasar,” in ji shi.