Bayanan da aka samu daga ƴan’uwa sun ce an sako Oba Clement Omoola Jimoh ne jiya Laraba, inda aka kai shi asibiti domin duba lafiyarsa.
A makon da ya gabata ne aka sace basaraken, inda ya kwashe mako guda a hannun masu garkuwa da mutane.
Lamarin ya faru ne a lokacin da ƴan bindigan suka kutsa fadarsa da ke ƙaramar hukuma Akoko ta Yamma a ranar Alhamis ɗin makon jiya, inda suka ɗauke shi zuwa wani wuri na daban.
Daga baya ƴan bindigan sun buƙaci a biya maƙudan kuɗaɗe domin sako shi, sai dai an sulhunta a kan ƙasa da abin da suka buƙata, amma duk da haka ba a fayyace ko sai da aka biya kuɗin fansar kafin sako basaraken ba.
Mai magana da yawun rundunar ƴan sandan Najeriya a jihar ta Ondo, SP Funmilayo Danlami ta tabbatar da lamarin a wata tattaunawa da kafar talabijin ta Channels.