fidelitybank

Basarake ya kubuta a hannun ‘yan ta’adda a Filato

Date:

An ceto Basaraken gargajiya mai daraja ta daya a Jihar Filato, Agwom Izere, Mai Martaba Dokta Isaac Azi Wakili, wanda wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba suka yi garkuwa da shi ranar Juma’a.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Filato, DSP Alfred Alabo, a wata sanarwa da ya fitar a yammacin ranar Juma’a, ya bayyana cewa jami’an rundunar sun kama wadanda suka sace basaraken.

A cewarsa: “An samu kiran tashin hankali daga hedikwatar ‘yan sanda ta Angware cewa wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba sun shiga fadar Agwom Izere da karfi, suka yi garkuwa da shi. Nan take jami’an ‘yan sanda karkashin jagorancin DPO na Angware, SP Timothy Bebissa, suka garzaya wurin da lamarin ya faru domin ceto sarkin, amma ‘yan bindigar sun yi artabu da bindiga, inda masu garkuwan suka harbe wani mai gadin farar hula da ba a tantance ba. kuma daya daga cikin ‘yan sandan ya samu rauni a harbin bindiga.”

Ya ce ’yan sanda da sauran jami’an tsaro da kungiyoyin sa kai sun yi dabara, inda suka dauki matakin ceto basaraken.

“An kuma kama wasu mutane biyu da ake zargi [da alaka da] wannan mugunyar,” in ji shi.

DSP Alabo ya ci gaba da cewa an kai jami’in da ya raunata asibiti yayin da aka ajiye gawar mai gadin farar hula a asibitin domin a tantance gawarwakin, yana mai jaddada cewa har yanzu ana ci gaba da gudanar da bincike domin kamo sauran ‘yan kungiyar da suka tsere.

cnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojojin hadin gwiwa sun hallaka ‘yan Boko Haram a tafkin Chadi

Rundunar hadin gwiwa mai yaƙi da Boko Haram a...

Na yi rashin aboki na gari kuma Najeriya ta rasa mutumin kirki – Tinubu

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, na ci gaba da alhinin...

Shettima ya jagoranci yi wa Buhari addu’o’i na musamman a Daura

An gudanar da addu'o'i na musamman don neman gafara...

Isra’ila ta kashe mana fararen hula – Syria

Shugaban Syria, Ahmed al-Sharaa ya zargi Isra'ila da kai...

Za mu koma fadar gwamnatin Katsina mu karbi gaisuwar Buhari – Radda

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umar Radda ya ce bayan...

Tinubu zai jagoranci yi wa Buhari addu’a

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, zai jagoranci taron addu'o'i na...

Muƙarraban Buhari sun ci amanar da ya ba su lokacin mulkinsa – Bagos

Wani tsohon ɗan majalisar wakilai, Dachung Bagos ya bayyana...

Guardiola ya bude kofa ga ‘yan wasa shida su bar kungiyar

Kocin Manchester City, Pep Guardiola, a shirye yake ya...

Ba gudu ba ja da baya a zanga-zangar mu – Tsofaffin ‘Yansanda

Kungiyar ‘yan sandan Najeriya masu ritaya ta sanar da...

Malami ya magantu kan sukar rashawa a mulkin marigayi Buhari

Tsohon babban Lauyan Najeriya kuma ministan shari'a, Abubakar Malami,...

Turkiyya ta gargadi Najeriya kan ‘yan ta’addar FETO

Gwamnatin Turkiyya ta fitar da wani gargadin cewa, mambobin...

Kiristoci sun jinjinawa Musulmai yadda aka yi jana’izar Buhari ba kashe kudi

Ana samun karuwar al’ummar Kudancin Najeriya musamman mabiya addinin...
X whatsapp