Mahukuntan Shahararriyar Kantin Tafkin Jabi da ke Abuja, sun rufe ayyukansu, sakamakon barazanar tsaro a babban birnin tarayya.
An bayyana hakan ne a ranar Alhamis a wani sako da aka wallafa a shafin sada zumunta na mall @jabilakemallnigeria.
Hukumar ta ce tana duba lamarin tsaro tare da hukumomin da suka dace kuma za a sake bude shi nan ba da jimawa ba.
Sanarwar dai na zuwa ne a daidai lokacin da rahotannin tsaro da Amurka da wasu kasashen yammacin duniya suka fitar na cewa ana fuskantar barazanar hare-haren ta’addanci a babban birnin tarayya Abuja.
Gargadin ya ce za a kai harin ne a kan gine-ginen gwamnati da wasu cibiyoyi da jama’a da dama ke taruwa
Sanarwar ta kara da cewa, “Ga dukkan masu siyayyar mu, Jabi Lake Mall za a rufe a yau, Alhamis, 27 ga Oktoba, 2022. An dauki wannan matakin ne don kare lafiyar dukkan ma’aikatan da abokan cinikin kantin.
“Cibiyar Gudanarwa ta himmatu wajen rage duk wani cikas; duk da haka, amincin ma’aikatanmu da masu siyayya ya kasance mafi fifikonmu. Hukumar gudanarwa na ci gaba da nazarin yanayin tsaro tare da tuntubar hukumomin tsaro da abin ya shafa kuma za su sanar da ku lokacin da za a sake bude kasuwar.
“Muna neman afuwar duk wata matsala da aka samu kuma muna fatan za mu samar muku da ingantacciyar hanyar siyayya nan ba da jimawa ba. Na gode.”