fidelitybank

Barazanar rufe Facebook ba zai hana mu hukunta kamfanin ba – FCCPC

Date:

Hukumar da ke sanya ido kan farashi da kare haƙƙin masu sayen kaya ta Najeriya (FCCPC), ta ce barazanar da kamfanin Meta ya yi na ficewa daga ƙasar, ba zai hana a hukunta shi ba.

Hukumar ta ce ba za a janye shari’ar da ake yi da Meta ba duk da barazanar da ya yi.

FCCPC ta ce kamfanin ya yi barazanar ficewa daga Najeriya ne domin a ji tausayinsa, da kuma matsawa hukumar canza matakin da ya ɗauka na cin tarar kamfanin.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da darektan hukumar, Ondaje Ijagwu ya fitar ranar Asabar.

Hakan kuma na zuwa ne bayan wani gargaɗi da Meta ya yi da farko cewa “za a tilasta masa rufe shafukan Facebook da Instagram a Najeriya don kauce wa barazanar fuskantar hukunci”.

Hukumar ta zargi Meta da yi wa bayanan ƴan ƙasar kutse, ciki har da aika bayanan ba tare da izininsu ba da rashin mutunta masu amfani da shafukan kamar yadda ake yi a sauran ƙasashe da kuma ɓullo da tsare-tsare da ba su da kyau kan ƴan ƙasar.

A bara ne hukumomin sanya ido uku na Najeriya suka lafta wa kamfanin tarar da ta kai fiye da dala miliyan 290, bisa zargin kamfanin da karya wasu dokoki.

sunnnewspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...
X whatsapp