fidelitybank

Barau zai mayar da filin wasan BUK na zamani

Date:

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya kammala shirin gyara da inganta tsarin ginin filin wasa na Jami’ar Bayero Kano (BUK), domin karɓar wasannin gasar kwallon kafa ta ƙasa da sauran manyan wasanni.

Wannan na zuwa ne jim kaɗan bayan da Barau FC, ƙungiyar kwallon kafa da Sanata Barau ya kafa, ta samu nasarar hawa daga Nigeria National League (NNL) zuwa Nigeria Premier Football League (NPFL). Wata tawaga daga ofishin Sanatan, wacce ta haɗa da Shugaban Ma’aikata, Farfesa Muhammad Ibn Abdallah; Mai Bada Shawara na Musamman kan Harkokin Yada Labarai, Alhaji Ismail Mudashir; da Mai Bada Shawara na Musamman kan Matasa da Wasanni, Kwamared Kabiru Ado Lakwaya, ta kai ziyara ga shugabancin jami’ar karkashin jagorancin Shugaban Jami’ar, Farfesa Haruna Musa, a ranar Talata.

Farfesa Abdallah, wanda ya jagoranci tawagar, ya bayyana cewa Sanatan ya ɗauki wannan mataki ne domin tabbatar da cewa BUK na da filin wasa na zamani da zai amfani jami’ar, al’ummarta, da kuma matasa masu sha’awar kwallon kafa. Da yake mayar da martani, Farfesa Musa ya gode wa Sanatan bisa wannan kyakkyawar manufa, yana mai cewa hakan ya yi daidai da tsare-tsaren da ya gabatar wa Majalisar Gudanarwa ta jami’ar lokacin da yake neman mukamin shugaban jami’ar. Ya kara da cewa jami’ar a shirye take ta ba da dukkan goyon baya don ganin an aiwatar da wannan aikin cikin nasara.

the nation newspaper 
today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Barau zai mayar da filin wasan BUK na zamani

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya...

Jami’ar Bayero ta Kano ta yi sabon shugaba

Farfesa Haruna Musa, ya karɓi ragamar shugabancin jami’ar Bayero...

Gwamnatin Kano ta amince Barau FC ta yi wasa a filin Sani Abacha

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da kungiyar kwallon kafa...

Gwamnatin Tinubu na takalar Kwankwaso da fada – Buba Galadima

Jigo a jam'iyyar NNPP, kuma na hannun tsohon gwamnan...

Newcastle United ta dauki dan wasan tsakiya Jacob daga Aston Villa

Newcastle United ta sanar da daukar dan wasan tsakiya...

Hisba ta kama ‘yan Mata 62 da zargin aikata baɗala a Kano

Hukumar Hisbah ta kama mutane 62 kan zargin aikata...

NNPP ta yi tafka magudi a zabencike gurbin Kano – Farouk Lawan

Tsohon dan majalisar wakilai, Farouk Lawan, ya yi zargin...

Dan shugaban kungiyar Boko Haram ya shiga hannu

Hukumomi a ƙasar Chadi sun kama yaron shugaban ƙungiyar...

Daga yau wankin koda a Najeriya ya koma dubu 12 maimakon dubu 50 – Tinubu

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya amince da rage farashin...

An ceto Mutane 25 da syka kife a kwale-kwalen Sokoto

Hukumomi a jihar Sokoto sun ce, sun samu nasarar...

An fara duba rabon gyaran arzikin Najeriya

Shugaban Hukumar rarraba arziƙin ƙasa RMAFC, Mohammed Shehu, ya...
X whatsapp