fidelitybank

Barau zai mayar da filin wasan BUK na zamani

Date:

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya kammala shirin gyara da inganta tsarin ginin filin wasa na Jami’ar Bayero Kano (BUK), domin karɓar wasannin gasar kwallon kafa ta ƙasa da sauran manyan wasanni.

Wannan na zuwa ne jim kaɗan bayan da Barau FC, ƙungiyar kwallon kafa da Sanata Barau ya kafa, ta samu nasarar hawa daga Nigeria National League (NNL) zuwa Nigeria Premier Football League (NPFL). Wata tawaga daga ofishin Sanatan, wacce ta haɗa da Shugaban Ma’aikata, Farfesa Muhammad Ibn Abdallah; Mai Bada Shawara na Musamman kan Harkokin Yada Labarai, Alhaji Ismail Mudashir; da Mai Bada Shawara na Musamman kan Matasa da Wasanni, Kwamared Kabiru Ado Lakwaya, ta kai ziyara ga shugabancin jami’ar karkashin jagorancin Shugaban Jami’ar, Farfesa Haruna Musa, a ranar Talata.

Farfesa Abdallah, wanda ya jagoranci tawagar, ya bayyana cewa Sanatan ya ɗauki wannan mataki ne domin tabbatar da cewa BUK na da filin wasa na zamani da zai amfani jami’ar, al’ummarta, da kuma matasa masu sha’awar kwallon kafa. Da yake mayar da martani, Farfesa Musa ya gode wa Sanatan bisa wannan kyakkyawar manufa, yana mai cewa hakan ya yi daidai da tsare-tsaren da ya gabatar wa Majalisar Gudanarwa ta jami’ar lokacin da yake neman mukamin shugaban jami’ar. Ya kara da cewa jami’ar a shirye take ta ba da dukkan goyon baya don ganin an aiwatar da wannan aikin cikin nasara.

besda

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp