fidelitybank

Barau ya karbi jiga-jigan mabiya bayan Shekarau zuwa APC

Date:

Mataimakin shugaban majalisar dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karbi bakuncin wasu dattawan jam’iyyar PDP masu biyayya ga tsohon gwamnan jihar Kano, Malam Ibrahim Shekarau a hukumance a lokacin da suka sauya sheka zuwa jam’iyyar All Progressives Congress (APC).

Sanata Barau ne ya bayyana hakan a shafin sa na Facebook da aka tabbatar.

“Na karbi tawagar dattawan jam’iyyar PDP, wadanda ke sansanin tsohon gwamnan jihar Kano, Malam Ibrahim Shekarau, zuwa babbar jam’iyyarmu – APC,” in ji Sanata Barau, wanda ke nuna wani gagarumin sauyi a fagen siyasar yankin.

Masu sauya shekar, karkashin jagorancin Hon. Lawan Abubakar Tsanyawa, ya hada da fitattun mutane kamar ’yan majalisar Shura, kwamandojin Hisbah, da tsaffin ‘yan majalisa, da tsaffin shugabannin kananan hukumomi. Sun bayyana ficewar su ne a lokacin da suka kai ziyara gidan Sanata Barau da ke Abuja. Karamin ministan gidaje da raya birane, Hon. Yusuf Abdullahi Ata shi ma ya shiga karbar kungiyar.

A nasa jawabin, Sanata Barau ya bayyana irin rawar da jam’iyyar APC ta taka wajen tsara shawarar da masu sauya shekar suka dauka, inda ya nuna gamsuwarsu da irin gudunmawar da jam’iyyar ke bayarwa wajen samar da ababen more rayuwa, karfafawa da samar da ayyukan yi a fadin yankin. “Ko da a matsayinsu na ‘yan PDP, sun ce sun amfana sosai daga ayyukan da muka yi a bangaren samar da ababen more rayuwa, karfafawa mutane, ayyukan yi, da sauran fannoni, hakan ne ya sa suka yanke shawarar komawa APC,” Barau ya bayyana.

Sanata Barau ya kuma tabbatar wa da sabbin ‘ya’yan jam’iyyar yadda za su shiga cikin jam’iyyar.

“Su ba baki bane a jam’iyyar APC, sun kasance mambobi ne kafin su bi shugabansu zuwa PDP, yanzu da muka sake haduwa za a yi musu adalci da daidaito,” inji shi.

A wani labarin kuma, Sanata Barau ya karbi bakuncin wata tawaga daga jam’iyyar New Nigeria People’s Party (NNPP) a karamar hukumar Bichi, karkashin jagorancin tsohon shugaban kansila, Alhaji Saleh Rabiu Yusuf (DanGwarzo).

‘Yan jam’iyyar NNPP sun bayyana tasirin ayyukan da jam’iyyar APC ke yi da kuma sahihancin shugabancin jam’iyyar a matsayin muhimman abubuwan da suka sa suka yanke shawarar shiga jam’iyya mai mulki.

nnn.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp