fidelitybank

Bankuna sun tsayar da aiki cak a Ondo

Date:

Bankunan kasuwanci sun dakatar da ayyukansu gaba daya a Akure babban birnin jihar Ondo.

Jaridar The Nation ta ruwaito cewa, dukkanin bankunan da wakilanta suka ziyarta a titin Oba Adesida da kuma Alagbaka a babban birnin jihar, kofofinsu na kulle.

Sai dai ta ce akwai tarin jama’a masu mu’amulla da bankin da suke tsaye curko-curko a wajen bankunan suna zaman jiran tsammani.

Daya daga cikin mutanen mai suna Jimoh ya bayyana cewa tun karfe 7:30 nsf (na safe) yake wurin.

Mutumin ya ce jami’an tsaron bankunan sun gaya masa cewa an rufe bankunan ne saboda tsoron kai musu hari.

kamar dai sauran sassan jihar ta Ondo can ma a garin Ikare-Akoko da ke yankin karamar hukumar Akoko Northeast ba a bude bankunan ba ga jama’a.

Jama’a na fama da wahalhalu sakamakon matakin Babban Bankin kasar na sauya fasalin wasu daga cikin manyan takardun kudin kasar na 1,000 da 500 da kuma 200.

Bankin ya sanya wa’adin daina karbar takardun a tsakanin jama’a zuwa ranar 10 ga watan nan na Fabrairu, to amma kuma a jiya laraba Kotun Kolin kasar ta yanke hukuncin shari’ar da gwamnonin jihohin Kogi da Kaduna da kuma Zamfara suka shigar gabanta kan hana wa’adin.

Kotun ta yanke hukuncin dakatar da aiwatar da shirin Bankin na hana mu’amulla da kudin har sai ta yanke hukunci na karshe a shari’ar wadda ta dage zuwa ranar 15 ga watan na Fabrairu.

thisday news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp