fidelitybank

Bankuna sun tsayar da aiki cak a Ondo

Date:

Bankunan kasuwanci sun dakatar da ayyukansu gaba daya a Akure babban birnin jihar Ondo.

Jaridar The Nation ta ruwaito cewa, dukkanin bankunan da wakilanta suka ziyarta a titin Oba Adesida da kuma Alagbaka a babban birnin jihar, kofofinsu na kulle.

Sai dai ta ce akwai tarin jama’a masu mu’amulla da bankin da suke tsaye curko-curko a wajen bankunan suna zaman jiran tsammani.

Daya daga cikin mutanen mai suna Jimoh ya bayyana cewa tun karfe 7:30 nsf (na safe) yake wurin.

Mutumin ya ce jami’an tsaron bankunan sun gaya masa cewa an rufe bankunan ne saboda tsoron kai musu hari.

kamar dai sauran sassan jihar ta Ondo can ma a garin Ikare-Akoko da ke yankin karamar hukumar Akoko Northeast ba a bude bankunan ba ga jama’a.

Jama’a na fama da wahalhalu sakamakon matakin Babban Bankin kasar na sauya fasalin wasu daga cikin manyan takardun kudin kasar na 1,000 da 500 da kuma 200.

Bankin ya sanya wa’adin daina karbar takardun a tsakanin jama’a zuwa ranar 10 ga watan nan na Fabrairu, to amma kuma a jiya laraba Kotun Kolin kasar ta yanke hukuncin shari’ar da gwamnonin jihohin Kogi da Kaduna da kuma Zamfara suka shigar gabanta kan hana wa’adin.

Kotun ta yanke hukuncin dakatar da aiwatar da shirin Bankin na hana mu’amulla da kudin har sai ta yanke hukunci na karshe a shari’ar wadda ta dage zuwa ranar 15 ga watan na Fabrairu.

latest news in nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Goodluck ya fi dacewa ya zama dan takara a 2027 – Lamido

Tsohon Gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido ya ce Tsohon...

An gargadi al’umma su yi taka tsan-tsan da ambaliyar ruwan sama

Yayin da ake ci gaba da fuskantar saukar ruwan...

Gwamnatin Tarayya za ta gina hanyar sufurin jirgin ƙasa a Kano

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta samar da titin...

Abin da ya sa muke ci gaba da tsare Sowore – Ƴansanda

Kwamishinan Æ´ansanda mai kula da sashen kai É—auki na...

INEC za ta bai wa É—aurarru damar kaÉ—a Æ™uri’a a lokacin zaÉ“uka

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta ta duba yiwuwar bai...

Mai ya jawo Matan Zamfara su ka yi zanga-zanga

ÆŠaruruwan mata ne tsofaffi da masu shawarya suka gudanar...

Aƙalla mutane 24,000 ne suka ɓata saboda Boko Haram a Najeriya

Kungiyar Agaji ta Red Cross ta bayyana cewa aƙalla...

‘Yansanda ku gaggauta sakin Sowore – Obi

Tsohon É—an takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP, Peter...

PDP ta gargaÉ—i mambobinta kan goyon bayan Tinubu

Babbar jam'iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ta gargaÉ—i...

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...
X whatsapp