fidelitybank

Bankuna na karkatar da sababbin kudade – Bankin Micro

Date:

Manajan Darakta na Bankin Micro Finance na Yobe ,Sheriff Muhammad Almuhajir, ya yi zargin cewa an karkatar da kudaden da babban bankin Najeriya CBN ya raba wa bankunan jihar da suka kai Naira biliyan 4.3.

MD ya yi wannan zargin ne a cikin wani hoton bidiyo na dakika 4:31 da ya wallafa a shafinsa na Facebook ranar Talata.

“Ina so in fada muku cewa, na samu tabbataccen labari cewa babban bankin Najeriya reshen Damaturu ya raba wa bankunan jihar Yobe zunzurutun kudi har naira biliyan 4.3.

Karanta Wannan: IMF ya roki CBN ya sakarwa ‘yan Najeriya mara

“Kuma sama da Naira miliyan 700 na kudin an yi wa jami’an P.O.S ne,” inji shi.

Almuhajir ya kuma yi zargin cewa Naira biliyan 4.3 da aka rabawa bankunan kasuwanci ba sa yaduwa a jihar, don haka ya zargi wasu manajojin bankin da karkatar da kudaden daga jihar.

“Amma tambayar da nake son yi anan ita ce, ina wannan kuɗaɗen?”, ya tambaya.

Ya yi zargin cewa sabbin takardun Naira da ake yawowa a fadin jihar ba su kai Naira biliyan daya ba.

MD na bankin ya bayar da hujjar cewa ko da ATMs za su rika ba da tsabar kudi a kowane minti daya, ba za a iya fitar da adadin a cikin mako guda ba.

“Nawa ne yawan al’ummar jihar Yobe?

“Bankunan kasuwanci nawa muke da su a jihar nan? ATM nawa muke da shi?” Ya tambaya.

Ya kara da cewa, jihar Yobe ba ta da injinan Automated Teller Machines, (ATMs) har guda 50, domin mutane su ciri N4.3. biliyan a cikin kankanin lokaci.

Almuhajir ya kuma bayar da hujjar cewa wasu ma’aikatan Points of Sale suna samar da ayyuka masu kyau fiye da yawancin bankunan kasuwanci da ke aiki a jihar.

latest news in nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Jihohi 19 da za a yi kwana 9 a na ruwan sama harda Kano – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta yi hasashen za a shafe kwana...

Tinubu ya mika sakon ta’aziyya bisa rasuwar matar MKO Abiola

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya miƙa saƙon ta'aziyyarsa bisa...

Abubuwan da Kwamiti ya gano a wajen Kwamishina mai murabus na Kano

A ranar Litinin ne kwamitin binciken badaƙalar belin Danwawu,...

Bajintar ɗaliban Najeriya a gasar Turanci ta nuna ingancin ilimi a ƙasa – Tinubu

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu, ya taya ƴanmatan nan uku...

Ƙudirin faɗaɗa mamayar Gaza zai ƙara jefa Falasɗinawa cikin hatsari – MDD

Majalisar Ɗinkin Duniya ta bayyana rahotannin da ke kwarmata...

APC a Kano mu na jinjinawa Tinubu – Abdullahi Abbas

Shugabannin jam’iyyar APC a jihar Kano, sun yabawa shugaba...

Kwamishinan da ake tuhuma da belin dilan kwayoyi a Kano ya yi murabus

Kwamishinan Sufuri na Jihar Kano, Ibrahim Ali Namadi ya...

Turji ya saki Mutane 32 bayan zaman sulhu

Shahararren shugaban ‘yan bindiga, Bello Turji, ya saki mutane...

ADC ta gargadi El’Rufa’i kan ruguza jam’iyyar

Shugaban jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) a jihar Kaduna,...

An gindayawa Thomas Partey sharudan beli

An gindaya sharuddan belin tsohon dan wasan tsakiya na...

Fursunoni 37 na jiran zartas musu da hukuncin kisa a Bauchi

Fursunoni 37 da aka yanke wa hukuncin kisa bisa...

Kwamitin sulhu na MDD zai gana kan makomar ƴan Isra’ila da ke hannun Hamas

Kwamitin tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya zai tattauna yau...
X whatsapp