fidelitybank

Bankuna na karkatar da sababbin kudade – Bankin Micro

Date:

Manajan Darakta na Bankin Micro Finance na Yobe ,Sheriff Muhammad Almuhajir, ya yi zargin cewa an karkatar da kudaden da babban bankin Najeriya CBN ya raba wa bankunan jihar da suka kai Naira biliyan 4.3.

MD ya yi wannan zargin ne a cikin wani hoton bidiyo na dakika 4:31 da ya wallafa a shafinsa na Facebook ranar Talata.

“Ina so in fada muku cewa, na samu tabbataccen labari cewa babban bankin Najeriya reshen Damaturu ya raba wa bankunan jihar Yobe zunzurutun kudi har naira biliyan 4.3.

Karanta Wannan: IMF ya roki CBN ya sakarwa ‘yan Najeriya mara

“Kuma sama da Naira miliyan 700 na kudin an yi wa jami’an P.O.S ne,” inji shi.

Almuhajir ya kuma yi zargin cewa Naira biliyan 4.3 da aka rabawa bankunan kasuwanci ba sa yaduwa a jihar, don haka ya zargi wasu manajojin bankin da karkatar da kudaden daga jihar.

“Amma tambayar da nake son yi anan ita ce, ina wannan kuɗaɗen?”, ya tambaya.

Ya yi zargin cewa sabbin takardun Naira da ake yawowa a fadin jihar ba su kai Naira biliyan daya ba.

MD na bankin ya bayar da hujjar cewa ko da ATMs za su rika ba da tsabar kudi a kowane minti daya, ba za a iya fitar da adadin a cikin mako guda ba.

“Nawa ne yawan al’ummar jihar Yobe?

“Bankunan kasuwanci nawa muke da su a jihar nan? ATM nawa muke da shi?” Ya tambaya.

Ya kara da cewa, jihar Yobe ba ta da injinan Automated Teller Machines, (ATMs) har guda 50, domin mutane su ciri N4.3. biliyan a cikin kankanin lokaci.

Almuhajir ya kuma bayar da hujjar cewa wasu ma’aikatan Points of Sale suna samar da ayyuka masu kyau fiye da yawancin bankunan kasuwanci da ke aiki a jihar.

nigeria.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp