fidelitybank

Bankin Duniya ya baiwa Najeriya tallafin dala miliyan 800

Date:

Najeriya ta samu tallafin dala miliyan 800 daga Bankin Duniya domin bunƙasa shirinta na zamantaƙewar al’ummar ƙasar gabanin cire tallafin man fetur a watan Yunin wannan shekara, a daidai lokacin da tattalin arzikin ƙasar ke tafiyar hawainiya.

Gwamnati ta ce za a raba kayan tallafin ne ta hanyar amfani da na’urar aika kuɗi ga ‘yan Najeriya kusan miliyan 50 ko gidaje miliyan 10, inda ta ce waɗannan mutane suna cikin mafi raunin rukunin al’umma.

Ta ce hakan na da nufin rage tasirin cire tallafin man fetur kan al’umma.

Bankin Duniya ya damu cewa ƙaruwar tattalin arzikin Najeriya da kashi 2.8 bai wadatar ba wajen rage sama da kashi 40 na al’ummar da ke fama da matsanancin talauci.

Najeriya da ta kasance ƙasa mafi tattalin arzikin a nahiyar Afirka, ta ware naira tiriliyan 3.36 a bana domin kashewa kan tallafin man fetur har zuwa tsakiyar shekara ta 2023 lokacin da za ta daina biya.

Najeriya ita ce ƙasa mafi yawan arzikin danyen mai a Afirka amma tana shigo da man fetur daga ƙasashen waje saboda rashin aiki da matatunta na mai ke yi.

nigeria news(punch)

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na ɗaukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa ƴan Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa ƴanbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen ƙauyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...
X whatsapp