fidelitybank

Bankin Duniya ya baiwa Najeriya tallafin dala miliyan 800

Date:

Najeriya ta samu tallafin dala miliyan 800 daga Bankin Duniya domin bunƙasa shirinta na zamantaƙewar al’ummar ƙasar gabanin cire tallafin man fetur a watan Yunin wannan shekara, a daidai lokacin da tattalin arzikin ƙasar ke tafiyar hawainiya.

Gwamnati ta ce za a raba kayan tallafin ne ta hanyar amfani da na’urar aika kuɗi ga ‘yan Najeriya kusan miliyan 50 ko gidaje miliyan 10, inda ta ce waɗannan mutane suna cikin mafi raunin rukunin al’umma.

Ta ce hakan na da nufin rage tasirin cire tallafin man fetur kan al’umma.

Bankin Duniya ya damu cewa ƙaruwar tattalin arzikin Najeriya da kashi 2.8 bai wadatar ba wajen rage sama da kashi 40 na al’ummar da ke fama da matsanancin talauci.

Najeriya da ta kasance ƙasa mafi tattalin arzikin a nahiyar Afirka, ta ware naira tiriliyan 3.36 a bana domin kashewa kan tallafin man fetur har zuwa tsakiyar shekara ta 2023 lokacin da za ta daina biya.

Najeriya ita ce ƙasa mafi yawan arzikin danyen mai a Afirka amma tana shigo da man fetur daga ƙasashen waje saboda rashin aiki da matatunta na mai ke yi.

www.nnn.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp