Shugaba Biden na Amurka ya ce, ba shi da wata nadama kan yadda Fadar Gwamnatin kasar, White House, ta yi game da batun bayyana cewa an samu takardun bayanan sirri na gwamnati a tsohon ofishinsa a Washington da kuma gidansa a Delaware.
Tun a watan Nuwamba da Disamba aka gano takardun, amma sai a farkon wannan watan nan aka bayyana labarin.
An nada jami’i na musamman domin gudanar da bincike kan yadda Mista Biden ya aikata hakan, wanda tun a lokacin yana mataimakin shugaban kasa ne a gwamnatin Obama.
Tsohon Shugaban Amurkar Donald Trump ma an gano tarin irin wadannan takardu na sirri a gidansa.