fidelitybank

Ban taɓa tsammanin zan shaƙi iskar ƴanci a mako guda ba – Ɗan Jarida

Date:

Abdulgafar Alabelewe, wakilin jaridar The Nation a Kaduna, an yi garkuwa da su kwanan nan kuma jami’an tsaron Najeriya suka ceto, a ranar Lahadin da ta gabata, ya ce bai taba tunanin zai shaki iskar ‘yanci cikin mako guda ba.

A makon jiya ne aka sace Alabelewe da Abdulraheem Aodu na jaridar Blueprint tare da ‘yan uwansu daga gidajensu na daban a Kaduna.

A wata sanarwa da Rabiu Ibrahim, mai taimakawa na musamman kan kafafen yada labarai ga ministan yada labarai da wayar da kan jama’a, Alabelewe ya mika godiyarsa ga mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro (NSA), Nuhu Ribadu da tawagarsa bisa gaggauwa da suka yi.

Ya bayyana cewa aikin ceto su da ya fitar da su daga cikin daji a ranar Asabar din da ta gabata ya ba su fata a kasar da kuma kwarin gwiwa kan yadda gwamnati za ta magance matsalar garkuwa da mutane, yana mai jaddada cewa bai taba tunanin za a ceto su cikin mako guda ba.

Ya ce, “Muna godiya ga gwamnati ta dauki matakin kuma ta tabbatar da cewa an sake mu.”

Ministan yada labarai da wayar da kan jama’a, Mohammed Idris, ya yi maraba da sakin ‘yan jarida biyu mazauna Kaduna, wadanda aka yi garkuwa da su daga gidajensu da ke wajen Kaduna a karshen mako.

tribune newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp