Mataimakin shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo ya ce, duk da bambancin addini, shi da shugaban kasa Muhammadu Buhari bai taba samun matsala ba tun hawansa mulki a shekarar 2015.
Osinbajo ya bayyana haka ne a wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Laolu Akande ya fitar.
Ya ce, “Shugaba Buhari musulmi ne mai kishin addini kuma ni Fasto ne; dukkanmu mun yi aiki tare har tsawon shekaru kusan bakwai; Ba mu samu matsala ba,”
“Dole ne mu yi amfani da imaninmu wajen inganta zaman lafiya da wadata ga mutanenmu; ya kamata mu hada kai don ganin al’ummarmu sun ci gajiyar addini,” inji shi.
“A wasu sassan duniya, shugabannin addini sun yi amfani da addini wajen kyautata rayuwar jama’a,” a cewar Osinbajo.
A shekarar 2019, an samu rahotannin cewa, Buhari da Osinbajo sun yi takun-saka yayin da aka bukaci shugaban da ya rika neman amincewar shugaban kasa a koda yaushe, domin tafiyar da hukumomin da ke ofishin sa. Har ila yau, akwai rahotannin da ke cewa, shugaban kasar ya kori akalla 35 daga cikin sama da hadimai 80 da ke ofishin Osinbajo.
Ko da wadannan rahotannin, mataimakin shugaban kasar ya bayyana Buhari a matsayin abin koyi na shugabanci da ke daukar mutane masu bambancin addini.
Mataimakin shugaban kasar ya bukaci malaman addini da su yi amfani da imani wajen samar da zaman lafiya, tabbatar da walwala ga al’umma da kuma ci gaban al’umma.