fidelitybank

Ban taba samun matsala da uban gidana ba – Osibanjo

Date:

Mataimakin shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo ya ce, duk da bambancin addini, shi da shugaban kasa Muhammadu Buhari bai taba samun matsala ba tun hawansa mulki a shekarar 2015.

Osinbajo ya bayyana haka ne a wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Laolu Akande ya fitar.

Ya ce, “Shugaba Buhari musulmi ne mai kishin addini kuma ni Fasto ne; dukkanmu mun yi aiki tare har tsawon shekaru kusan bakwai; Ba mu samu matsala ba,”

“Dole ne mu yi amfani da imaninmu wajen inganta zaman lafiya da wadata ga mutanenmu; ya kamata mu hada kai don ganin al’ummarmu sun ci gajiyar addini,” inji shi.

“A wasu sassan duniya, shugabannin addini sun yi amfani da addini wajen kyautata rayuwar jama’a,” a cewar Osinbajo.

A shekarar 2019, an samu rahotannin cewa, Buhari da Osinbajo sun yi takun-saka yayin da aka bukaci shugaban da ya rika neman amincewar shugaban kasa a koda yaushe, domin tafiyar da hukumomin da ke ofishin sa. Har ila yau, akwai rahotannin da ke cewa, shugaban kasar ya kori akalla 35 daga cikin sama da hadimai 80 da ke ofishin Osinbajo.

Ko da wadannan rahotannin, mataimakin shugaban kasar ya bayyana Buhari a matsayin abin koyi na shugabanci da ke daukar mutane masu bambancin addini.

Mataimakin shugaban kasar ya bukaci malaman addini da su yi amfani da imani wajen samar da zaman lafiya, tabbatar da walwala ga al’umma da kuma ci gaban al’umma.

legit news 
nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp