fidelitybank

Ban taba fargabar Tinubu zai kore ni daga kujera ta ba – Minista

Date:

Ministar fasaha da raya al’adu ta kasa, Hannatu Musawa, ta ce ba ta damu da batun shirin da shugaban ƙasar Bola Ahmed Tinubu ke yi ba na yin garambawul a majalisar zartarwarsa.

Ministar ta bayyana haka ne a cikin shirin siyasa na gidan talabijin na Channels a jiya Lahadi.

An tambayi ministar ko tana fargabar Shugaba Tinubu zai iya cire ta idan aka yi la’akari da cecekucen da ya mamaye ta bayan ba ta muƙamin minista?

Sai ta ce: “Ba ni tunanin akwai wani cecekuce da ya dabaibaye naɗina da kuma ofishina. Abin da za ni ce shi ne, na yi wa Shugaba Tinubu kamfe domin ya zama shugaban ƙasa, saboda haka na amince da duk matakin da zai ɗauka.

“Ban damu ba saboda na san cewa ci gaban ƙasa ne a gaban shugaba Bola Ahmed Tinubu, don haka duk matakin da zai ɗauka wajen yin garambawul a gwamnatinsa zai zama mai amfani ga ƴan Najeriya.

An daɗe ana kiraye-kiraye ga shugaban Najeriya da ya sauya wasu daga cikin ministocinsa saboda ana ganin ba su yin abin da ya dace.

A ƙarshen watan da ya gabata, mai magana da yawun shugaban ƙasar, Bayo Onanuga ya ce shugaban ya bayyana kudurinsa na yin garambawul ga majalisar zartarwarsa, sai dai ba a bayyana lokaci ba.

besda

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp