Tsohon kwamishinan zaɓen jihar Adawama, Hudu Ari – da aka sauke a baya-bayan nan bisa zargin aikata laifukan zaɓe, ya bayyana damuwarsa kan rashin ba shi dama kan zargin da ake yi masa kafin ɗaukar cire shi daga matsayinsa.
Yayin da yake magana da manema labarai a Bauchi, Ari ya yi iƙirarin cewa ya rubuta wasiƙu da dama ga hukumar zaɓen ƙasar, domin bayyana mata ainihin abin da ya sani kan zargin da ake yi masa, amma sai hukumar ta yi watsi da wasiƙun nasa.
Ya ƙara da cewa kotun – da ta saurari ƙarar zaɓe tsakanin tsohuwar ‘yar takarar gwamnan jihar Adamawa a jam’iyyar APC, Sanata Aishatu Binani da kuma gwamnan jihar Ahmadu Fintiri – ta ƙi amincewa da shaidarsa.
A 2023 ne lokacin da ake dakon sakamakon ƙarshe a zaɓen gwamnan jihar Adamawa, kwamishinan zaɓen jihar, Hudu Ari – wanda a doka ba shi ne da alhakin faɗin sakamakon zaɓe ba – ya bayyana ‘yar takarar APC, Aishatu Binani a matsayin wadda ta lashe zaɓen.
Wani lamari da ya tayar da yamutsi da tashin hankali a jihar.
To sai dai Ari ya dage cewa yana da ƙwararan hujjojin da suka sanya shi ɗaukar matakin, amma ba a gayyace shi kotun domin gabatar da su ba.
Ya ce korar da aka yi masa ba ta ɓata masa rai ba, kamar rashin ba shi damar kare kansa bisan zargin da ake yi masa.
”Aikin gwamnati wani abu ne mai cike da tsari, da dokoki da ƙa’idoji, bisa doka ya kamata a saurareni. Kuma ko Ubangiji ma ai ba zai hukunta ka ba har sai ya turo maka ɗan aike, manzanni da littattafai, kuma ka saɓa”, kamar yadda ya bayyana.
Tsohon kwamishinan ya ce bai taɓa yin nadamar abin da ya aikata ba, saboda duk abin da yi a bisa doron gaskiya yake