fidelitybank

Ban taɓa yin nadamar ayyana Binani a matsayin gwamnan Adamawa ba – Hudu Ari

Date:

Tsohon kwamishinan zaɓen jihar Adawama, Hudu Ari – da aka sauke a baya-bayan nan bisa zargin aikata laifukan zaɓe, ya bayyana damuwarsa kan rashin ba shi dama kan zargin da ake yi masa kafin ɗaukar cire shi daga matsayinsa.

Yayin da yake magana da manema labarai a Bauchi, Ari ya yi iƙirarin cewa ya rubuta wasiƙu da dama ga hukumar zaɓen ƙasar, domin bayyana mata ainihin abin da ya sani kan zargin da ake yi masa, amma sai hukumar ta yi watsi da wasiƙun nasa.

Ya ƙara da cewa kotun – da ta saurari ƙarar zaɓe tsakanin tsohuwar ‘yar takarar gwamnan jihar Adamawa a jam’iyyar APC, Sanata Aishatu Binani da kuma gwamnan jihar Ahmadu Fintiri – ta ƙi amincewa da shaidarsa.

A 2023 ne lokacin da ake dakon sakamakon ƙarshe a zaɓen gwamnan jihar Adamawa, kwamishinan zaɓen jihar, Hudu Ari – wanda a doka ba shi ne da alhakin faɗin sakamakon zaɓe ba – ya bayyana ‘yar takarar APC, Aishatu Binani a matsayin wadda ta lashe zaɓen.

Wani lamari da ya tayar da yamutsi da tashin hankali a jihar.

To sai dai Ari ya dage cewa yana da ƙwararan hujjojin da suka sanya shi ɗaukar matakin, amma ba a gayyace shi kotun domin gabatar da su ba.

Ya ce korar da aka yi masa ba ta ɓata masa rai ba, kamar rashin ba shi damar kare kansa bisan zargin da ake yi masa.

”Aikin gwamnati wani abu ne mai cike da tsari, da dokoki da ƙa’idoji, bisa doka ya kamata a saurareni. Kuma ko Ubangiji ma ai ba zai hukunta ka ba har sai ya turo maka ɗan aike, manzanni da littattafai, kuma ka saɓa”, kamar yadda ya bayyana.

Tsohon kwamishinan ya ce bai taɓa yin nadamar abin da ya aikata ba, saboda duk abin da yi a bisa doron gaskiya yake

thisday nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...
X whatsapp