fidelitybank

Ban taɓa cin zarafin Sanata Natasha ba – Akpabio

Date:

Shugaban Majalisar Dattijan Najeriya, Godswill Akpabio ya musanta zargin da ɗaya daga cikin sanatoci mata ta ƙasar, Natasha Akpoti ta yi kan cewa ya taɓa yunƙurin cin zarafinta ta hanyar lalata.

Akpabio ya bayyana hakan ne a farkon zaman majalisar na yau Laraba.

Akpabio ya ce “ina son shaida wa duniya cewa ban taɓa cin zarafin Sanata Natasha ko wata mace ba…mahaifiyata ta yi min tarbiyya mai kyau, saboda haka ina girmama mata”.

Kalaman shugaban Majalisar Dattaijan na zuwa ne bayan Sanata Natasha Akpoti ta gabatar da ƙorafinta ga majalisar game da zargin yunƙurin cin zarafi da take yi wa Akpabio.

Batun dai ya janyo muhawara mai zafi a faɗin Najeriya, tun bayan da Sanatar ta bayyana a wata tattaunawa da kafar talabijin ta Arise, cewa Akpabio ya faɗa mata wasu kalamai da ba su dace ba.

Ƙungiyoyi da dama ne suka buƙaci a gudanar da cikakken bincike kan lamarin, yayin da wasu kuma ke ganin cewa bai kamata a ci gaba da tattaunawa kan lamarin ba.

A zaman majalisar na yau Laraba an tafka muhawara inda wasu sanatocin suka mike suka bayyana cewa bai kamata a saurari ƙorafin Natasha ba kasancewar ta shigar da ƙara a gaban kotu.

Sai dai Natasha ta kare matakin nata, inda ta ce ƙarar da ta shigar a kotu ta shafi batun ɓata suna ne da wani hadimin Sanata Akpabio ya yi, yayin da ƙorafinta ga majalisar kuma ya shafi batun yunƙurin cin zarafin lalata ne da take zargin shugaban majalisar da aikatawa.

daily sun news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da...

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...
X whatsapp