fidelitybank

Ban taɓa cin zarafin Sanata Natasha ba – Akpabio

Date:

Shugaban Majalisar Dattijan Najeriya, Godswill Akpabio ya musanta zargin da ɗaya daga cikin sanatoci mata ta ƙasar, Natasha Akpoti ta yi kan cewa ya taɓa yunƙurin cin zarafinta ta hanyar lalata.

Akpabio ya bayyana hakan ne a farkon zaman majalisar na yau Laraba.

Akpabio ya ce “ina son shaida wa duniya cewa ban taɓa cin zarafin Sanata Natasha ko wata mace ba…mahaifiyata ta yi min tarbiyya mai kyau, saboda haka ina girmama mata”.

Kalaman shugaban Majalisar Dattaijan na zuwa ne bayan Sanata Natasha Akpoti ta gabatar da ƙorafinta ga majalisar game da zargin yunƙurin cin zarafi da take yi wa Akpabio.

Batun dai ya janyo muhawara mai zafi a faɗin Najeriya, tun bayan da Sanatar ta bayyana a wata tattaunawa da kafar talabijin ta Arise, cewa Akpabio ya faɗa mata wasu kalamai da ba su dace ba.

Ƙungiyoyi da dama ne suka buƙaci a gudanar da cikakken bincike kan lamarin, yayin da wasu kuma ke ganin cewa bai kamata a ci gaba da tattaunawa kan lamarin ba.

A zaman majalisar na yau Laraba an tafka muhawara inda wasu sanatocin suka mike suka bayyana cewa bai kamata a saurari ƙorafin Natasha ba kasancewar ta shigar da ƙara a gaban kotu.

Sai dai Natasha ta kare matakin nata, inda ta ce ƙarar da ta shigar a kotu ta shafi batun ɓata suna ne da wani hadimin Sanata Akpabio ya yi, yayin da ƙorafinta ga majalisar kuma ya shafi batun yunƙurin cin zarafin lalata ne da take zargin shugaban majalisar da aikatawa.

kano news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...
X whatsapp