Dan takarar shugaban kasa na jamâiyyar All Progressives Congress (APC) mai mulki, Bola Tinubu, ya ce, bai sanar da tsohon gwamnan jihar Borno, Sanata Kashim Shettima ba, cewa an zabe shi a matsayin wanda zai tsaya takara.
Tsohon gwamnan na Legas ya bayyana haka ne a ranar Lahadin da ta gabata yayin wata tattaunawa da manema labarai bayan ganawar sirri da ya yi da shugaban kasa Muhammadu Buhari a garin Daura na jihar Katsina.
Tinubu ya bayyana cewa, ya kuma sanar da dan takarar mataimakin shugaban kasa na rikon kwarya, Kabir Ibrahim Masari, matakin da ya dauka na maye gurbinsa da Shettima a matsayin abokin takararsa a hukumance.
Ya ce, âNa ga Kabir Ibrahim Masari a yau kuma za a fitar da sanarwar maye gurbinsa da cikakken dan takara.â
Da aka tambaye shi ya bayyana ko wanene dan takarar, Tinubu ya bayyana cewa Shettima ne, duk da cewa bai tattauna da shi ba.
“Kashim Shettima, ban tattauna da shi ba amma na bayyana maka,” in ji shi.
Sanarwar ta Tinubu ta zo ne kasa da saâa guda bayan Masari ya sauka daga mukamin mataimakin shugaban kasa a hukumance.