fidelitybank

Ban san da kama Yara masu zanga-zanga ba – Gwamnan Kano

Date:

Gwamnan jihar Kano, Abba Yusuf, ya ce bai san da kama yaran ba har sai an gurfanar da su a gaban babbar kotun tarayya da ke Abuja.

Yusuf ya bayyana haka ne a asibitin Muhammadu Buhari, inda aka tura tawagar kwararrun likitocin domin tantance lafiyar yara 76 da aka sako.

Ya nuna godiya ga shugaban kasa Bola Tinubu, inda ya nuna jin dadinsa ga yaran.

“Da samun labarin lamarin, nan take na umurci babban mai shari’a da kuma kwamishinan shari’a da ya dauki nauyin lamarin.

“Ina kuma mika godiyata ga duk wanda ke da hannu wajen tabbatar da dawowar kananan yara lafiya.

“Ina kuma yaba wa iyaye bisa ga addu’o’in da suka yi da kuma nuna balaga a cikin wannan mawuyacin lokaci, a lokacin da kuma bayan sakin kananan yara da abin ya shafa.

“Natsuwarsu da juriyarsu abin burgewa ne,” in ji shi.

Gwamnan ya bada tabbacin cewa gwamnatin sa za ta yi duk mai yiwuwa na dan Adam wajen hada yaran da iyayensu tare da ba su tallafin da ya kamata domin yin kananan sana’o’i.

Ya kuma jaddada mahimmancin ilimi, tare da tabbatar da cewa yaran sun koma makaranta domin bayar da gudunmawar ci gaban jihar.

A cewarsa, gwamnatin jihar za ta dauki matakin mayar da kananan yaran da aka kama a kan zanga-zangar #EndBadGovernance.

latest news in nigeria today 2022 punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp