Gwamnan jihar Sokoto, Aminu Tambuwal ya karyata rahotannin da ke cewa, ya karkatar da Naira biliyan 198.
Gwamnan ya karyata rahotannin ne ta wata sanarwa mai dauke da sa hannun mai taimaka masa na musamman kan harkokin yada labarai, Muhammad Ahmad Bello.
Sanarwar ta ci gaba da cewa: “Hankalin mu ya karkata ga rahotannin rashin gaskiya da tsokana da wasu sabbin kafafen yada labarai na yanar gizo ke yi kan zargin karkatar da Naira biliyan 189 da gwamnatin Jihar Sokoto ta yi.
“Rahotanni sun yi nuni da wani abin da ake kira rahoton rikon kwarya na EFCC kan Jihar Sokoto. Waɗannan rahotannin kafofin yaɗa labaru karya ne a cikin duk bayanan kayan aiki, kuma yakamata a yi watsi da su gaba ɗaya.
“Muna fadakar da jama’a cewa, wadannan rahotannin da kafafen yada labarai suka bayar na kokarin bata sunan Gwamna, Aminu Tambuwal, wanda ke kan gaba wajen neman tikitin takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a 2023.
“Gwamnatin jihar Sokoto ta kafa martabar da ta dace a matsayin mai fafutukar tabbatar da kasafin kudi, alhakin kasafin kudi, da gudanar da mulki a fili. Mun yi rajista ga Budaddiyar hulda da Jama’a (OGP).