Gwamnatin jihar Ribas ta musanta cewa, ta damke mambobin kungiyar yakin neman zaben Atiku Abubakar su 30 a Fatakwal.
Atiku, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, da gwamnan Rivers, sun shiga takun saka tun bayan zaben fidda gwani na jam’iyyar.
Rahotanni sun bayyana a ranar Lahadin da ta gabata cewa, ‘yan sanda dauke da makamai sun cafke kusan mambobin kungiyar yakin neman zaben su 30 a wani taro a Fatakwal.
Karanta Wannana: Wike ya zama matsoraci ya kasa bayyana dan takara – Dakuku
Kakakin kungiyar kamfen, Victor Moses, ya ce wasu daga cikin wadanda aka kama shugabannin kungiyar ne na jiha da na kananan hukumomi.
Kakakin yakin neman zaben ya yi zargin cewa jami’an ‘yan sanda sun yi aiki da umarnin Wike, wanda ya sha alwashin yin aiki da Atiku a zabe mai zuwa.
Sai dai kwamishinan yada labarai na jihar Ribas, Chris Finebone, yayin da yake mayar da martani kan wannan zargi a ranar Litinin, ya ce rashin hankali ne kungiyar yakin neman zaben Atiku ta alakanta Gwamna Wike da batutuwan da suke da ita da ‘yan sanda.
Da yake musanta rahoton, Finebone ya shaidawa gidan talabijin na Channels cewa zargin na daya daga cikin abubuwan da mutane ke ganin ya dace su nuna yatsa ga gwamnatin da ke mulki.