fidelitybank

Ban kama magoya bayan Atiku ba – Wike

Date:

Gwamnatin jihar Ribas ta musanta cewa, ta damke mambobin kungiyar yakin neman zaben Atiku Abubakar su 30 a Fatakwal.

Atiku, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, da gwamnan Rivers, sun shiga takun saka tun bayan zaben fidda gwani na jam’iyyar.

Rahotanni sun bayyana a ranar Lahadin da ta gabata cewa, ‘yan sanda dauke da makamai sun cafke kusan mambobin kungiyar yakin neman zaben su 30 a wani taro a Fatakwal.

Karanta Wannana: Wike ya zama matsoraci ya kasa bayyana dan takara – Dakuku

Kakakin kungiyar kamfen, Victor Moses, ya ce wasu daga cikin wadanda aka kama shugabannin kungiyar ne na jiha da na kananan hukumomi.

Kakakin yakin neman zaben ya yi zargin cewa jami’an ‘yan sanda sun yi aiki da umarnin Wike, wanda ya sha alwashin yin aiki da Atiku a zabe mai zuwa.

Sai dai kwamishinan yada labarai na jihar Ribas, Chris Finebone, yayin da yake mayar da martani kan wannan zargi a ranar Litinin, ya ce rashin hankali ne kungiyar yakin neman zaben Atiku ta alakanta Gwamna Wike da batutuwan da suke da ita da ‘yan sanda.

Da yake musanta rahoton, Finebone ya shaidawa gidan talabijin na Channels cewa zargin na daya daga cikin abubuwan da mutane ke ganin ya dace su nuna yatsa ga gwamnatin da ke mulki.

latest news nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...
X whatsapp