Shugaba Bola Tinubu ya nuna ɓacin-rai da kuma kaɗuwa kan kashe mutane da wasu ƴan bindiga suka yi a ƙaramar hukumar Bassa ta jihar Filato.
Shugaban ya yi Alla-wadai da lamarin, ya kuma miƙa ta’aziyyarsa ga al’ummar jihar – inda ya buƙaci a nemi hanyar warware rikicin da kuma samar da zaman lafiya.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban Bayo Onanuga ya fitar, inda Tinubu ya nanata muhimmancin haɗin-kai ba tare da nuna bambacin addini ko kabila.
“Dole ne shugabannin al’ummomi da na addini da kuma siyasa su zo su haɗa-kai don daƙile waɗannan hare-hare da suka addabi jama’a,” in ji Tinbu.
Aƙalla mutum 50 ne suka mutu a harin da ƴan bindigar suka kai jihar a cikin daren Litinin.