Bayan tsawon lokaci ba a ji ta bakinsa ba dangane da faruwar al’amuran siyasa, tsohon shugaban Najeriya, Goodluck Ebele Jonathan ya ɓara inda ya yi gargaɗin cewa “abu ne mai haɗari ɗora Najeriya a kan turbar jam’iyya guda ɗaya”.
Ba kasafai dai ake jin bakin Goodluck Jonathan ba a al’amura kasancewarsa mutum mai kawaici da rashin son yawan magana.
To sai dai a ranar Larabar nan, tsohon shugaban na Najeriya yayin wata lacca da aka shirya a Abuja domin tuna wa da marigayi Edwin Clerk, dattijo ɗan ƙabilar Ijaw wanda ya rasu yana da shekara 97, Jonathan ya ja hankalin gwamnati da jam’iyya mai mulki ta APC da ake zargi da mayar da ƙasar ƙarƙashin tsarin jam’iyya guda.