Babban mai kula da cocin Citadel Global Community Church, Tunde Bakare, ya musanta rahotannin da ke cewa ya amince da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress (APC), Bola Ahmed Tinubu.
A wata sanarwa da cocin ta raba wa manema labarai a jiya Juma’a 22 ga watan Yuli, 2022, Bakare ya karyata kalaman da wasu jaridu suka yi masa na cewa ya amince da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC.
Tsohon dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar APC ya kuma musanta wasu kalamai marasa dadi game da kungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN), kungiyar Kiristoci a Najeriya.
Sanarwar ta ci gaba da cewa, “ Hankalina ya karkata ga labarin da ake yadawa, amma na kumbiya-kumbiya da ba’a da wasu marasa kishin marubuta da masu rubutun ra’ayin yanar gizo suka yi min. Daga cikin abubuwan da aka jiyo na na cewa tada hankalin kungiyar Kiristocin Najeriya, CAN, wata dabara ce da jam’iyyar adawa ta PDP ta yi na tilasta wa dan takara mai rauni a jam’iyyar APC. An yi zargin cewa CAN ta so ta jawo APC ta gabatar da dan takara mai rauni.