Babban Sufeton ƴansanda na ƙasa, Kayode Egbetokun, ya haramta wa ƙungiyar tsaro ta jihohin kudu maso yamma da ake wa lakabi da Amotekun da ‘yansintiri na Vigilante da sauran ire-irensu shiga harkokin zaɓen gwamnan jihar Ondo.
A wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yansandan na ƙasa Auyiwa Adejobi ya fitar a yau Lahadi, ya ce Babban Sufeton ya bayar da umarnin tura jami’an ‘yansanda daga ɓangarori daban-daban na rundunar domin aikin zaɓen.
Aƙalla jam’iyyu 17 ne aka bayar da rahoton cewa za su shiga zaɓen wanda za a yi ranar Asabar mai zuwa, 16 ga watan Nuwamba, 2024.
Sanarwar ta ce ‘yansanda da sauran hukumomin tsaro na tarayya ne za su aikin tabbatar da tsaro a lokacin.