Gwamnan Borno Farfesa Babagana Umara Zulum ya yi watsi da sunansa da aka saka a ginin wasu ɗakunan kwanan ɗalibai a Kwalejin fasaha ta Ramat a Maiduguri na gwamnatin jihar.
Zulum ya yi watsi da karamcin ne lokacin da yake ƙaddamar da ginin da ma’aikatar ilimi ta gyara.
A sanarwar da gwamnatin Borno ta fitar, Zulum ya ce “Ba zan yarda a saka sunana a wani aikin gwamnati ba, a lokacin da nake kan mulki. Ya kamata ko za a yi sai na gama wa’adi na.”
Maimakon sunansa, gwamna Zulum ya buƙaci a sauya zuwa “ɗakin kwanan ɗalibai maza.”