Hukumar ba da tallafin karatu ta Jihar Sokoto, ta ce, ta samu wata wasika daga jamiāar ISMU ta kasar Rasha da ke cewa, ikirarin da dalibin nan dan asalin jihar Yahaya Usman ya yi cewa, an kore shi daga makarantar kuma yana tsare a sansanin tsare bakin Haure ba gaskiya ba ne.
A cikin wasikar wadda BBC ta ga Kofenta dauke da san hannun Babbar Jamiāa mai kula da hulda da daliban kasashen wajen Elena Orel, jamiāar ta ce duk da cewa lalle ana bin dalibin bashin kudin karatu; yana nan a sake kuma yana zuwa aji don daukar darasi.
A makonnin baya ne dai dalibin ya yi ta hira da kafafen watsa labarai yana zargin cewa an kore shi daga makaranta kuma an tsare a sansanin tsare bakin haure saboda kasawar hukumomin jiharsa na biya masa kudin karatu.
Alhaji Bello Isah shi ne babban sakatare a hukumar ba da tallafin karatun ta jihar Sakkwato, kuna iya sauraronkarin bayanin da ya yi wa BBC.