fidelitybank

Bamu kama maharan da suka kai hari Cocin Owo ba – ‘Yan sanda

Date:

Rundunar ‘yan sandan Jihar Ondo ta musanta rahotannin da ke cewa, ta kama maharan da suka kashe masu ibada fiye da 40 a harin da suka kai Cocin Katolika ta St. Francis a jihar.

Rahotannin da aka dinga yaɗawa a shafukan zumunta sun bayyana cewa, dakarun haɗin gwiwa na sojoji ne da ‘yan sanda da na rundunar Amotekun suka kama maharan a ranar Alhamis.

Sannan sun yi iƙirarin cewa an kai mutanen fadar Mai Martaba Olowo na Owo Oba Ajibade Ogunoye, inda mutane suka yi tururuwa don ganin waɗanda ake zargin.

Sai dai basaraken ya musanta batun kamen yayin hirarsa da jaridar Punch a yau Juma’a. “Rahoton ba gaskiya ba ne,” in ji shi. “Mutane sun yi ta zuwa fada don ganin su amma Olowo ya faɗa musu babu wanda aka kawo fadar.”

Ita ma kakakin rundunar ‘yan sandan Ondo, Funmilayo Odunlami, ta ce babu wanda aka kama da zargin kai harin na ranar Lahadi da ta wuce.

Gwamnatin Najeriya ta ce ƙungiyar ISWAP mai alaƙa da ƙungiyar masu iƙirarin jihadi ta Islamic State (IS) ce ta kai harin. In ji BBC.

www.legit.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...
X whatsapp