Rundunar ‘yan sandan Jihar Ondo ta musanta rahotannin da ke cewa, ta kama maharan da suka kashe masu ibada fiye da 40 a harin da suka kai Cocin Katolika ta St. Francis a jihar.
Rahotannin da aka dinga yaɗawa a shafukan zumunta sun bayyana cewa, dakarun haɗin gwiwa na sojoji ne da ‘yan sanda da na rundunar Amotekun suka kama maharan a ranar Alhamis.
Sannan sun yi iƙirarin cewa an kai mutanen fadar Mai Martaba Olowo na Owo Oba Ajibade Ogunoye, inda mutane suka yi tururuwa don ganin waɗanda ake zargin.
Sai dai basaraken ya musanta batun kamen yayin hirarsa da jaridar Punch a yau Juma’a. “Rahoton ba gaskiya ba ne,” in ji shi. “Mutane sun yi ta zuwa fada don ganin su amma Olowo ya faɗa musu babu wanda aka kawo fadar.”
Ita ma kakakin rundunar ‘yan sandan Ondo, Funmilayo Odunlami, ta ce babu wanda aka kama da zargin kai harin na ranar Lahadi da ta wuce.
Gwamnatin Najeriya ta ce ƙungiyar ISWAP mai alaƙa da ƙungiyar masu iƙirarin jihadi ta Islamic State (IS) ce ta kai harin. In ji BBC.