A ranar Asabar din da ta gabata ne Majalisar ba da Shawarar ta Jam’iyyun siyasa, Inter Party (IPAC) ta yi watsi da shawarar Hukumar Yaki da Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Kasa (NDLEA) na cewa, jam’iyyun siyasa su sanya gwajin ingancin muggan kwayoyi cikin sharuddan tantance masu neman tsayawa takarar mukaman siyasa a zaben 2023.
IPAC ta bayyana matakin a matsayin rashin kunya, rashin sanin yakamata, rashin gaskiya, kai hari da gangan ga masu son mulkin dimokaradiyya a Najeriya.
Majalisar ta ce, shawarar ta nuna ‘yan siyasa a matsayin masu shaye-shayen miyagun kwayoyi wadanda dole ne a ba su shaidar cancantar tsayawa takarar mukamai daban-daban a hukumar.
Wata sanarwa da shugaban kungiyar IPAC na kasa Engr. Yabagi Yusuf Sani ya ce: “Abin zargi ne kuma ba za a yarda da shi ba. IPAC ta bukaci NDLEA ta nemi afuwarta tare da gargadin hukumar yaki da miyagun kwayoyi da kakkausar murya da ta daina tozarta halayya da mutuncin ‘yan siyasa ciki har da wadanda ke takarar shugaban kasa masu kishin kasa, mutuntawa, jiga-jigan jahohi da mata da suka tabbatar da gaskiya. Kamata ya yi a sami iyaka ga wariyar launin fata wajen gudanar da ayyukan jama’a.