An sami fashewar wani abu daddare wanda ya haddasa tashin hankali a garin Gashua na jihar Yobe.
Al’ummar da shugaban majalisar dattawa, Sanata Ahmed Lawan ya fito sun shiga cikin fargaba a daren Lahadi, bayan da wata na’urar da ba a tantance ba ta fashe, inji rahoton Naija News Hausa.
Gashua na cikin karamar hukumar Bade, kimanin kilomita 188 daga Damaturu, babban birnin jihar Yobe.
Fashewar daren Lahadi a cewar rahotanni, ya afku ne a wani wurin shan giya da ke unguwar Abasha a garin a lokacin da musulmin ke gudanar da sallar magariba.
Wani mazaunin al’ummar da ya shaida wa Daily Post, ya ce suna Sallah ne a masallatai da misalin karfe 8 na dare, sai suka ji karar fashewar bam din da ake zargin bama-bamai ne.
Rahotanni sun ce mutum daya ya mutu a lamarin yayin da wasu akalla bakwai suka samu raunuka daban-daban.
Nan take aka garzaya da su Asibitin Kwararru da ke Gashua domin jinya, kamar yadda majiyar da ta nemi a sakaya sunanta ta shaida wa manema labarai.