fidelitybank

Bam ya tashi a yankin shugaban majalisar dattijai

Date:

An sami fashewar wani abu daddare wanda ya haddasa tashin hankali a garin Gashua na jihar Yobe.

Al’ummar da shugaban majalisar dattawa, Sanata Ahmed Lawan ya fito sun shiga cikin fargaba a daren Lahadi, bayan da wata na’urar da ba a tantance ba ta fashe, inji rahoton Naija News Hausa.

Gashua na cikin karamar hukumar Bade, kimanin kilomita 188 daga Damaturu, babban birnin jihar Yobe.

Fashewar daren Lahadi a cewar rahotanni, ya afku ne a wani wurin shan giya da ke unguwar Abasha a garin a lokacin da musulmin ke gudanar da sallar magariba.

Wani mazaunin al’ummar da ya shaida wa Daily Post, ya ce suna Sallah ne a masallatai da misalin karfe 8 na dare, sai suka ji karar fashewar bam din da ake zargin bama-bamai ne.

Rahotanni sun ce mutum daya ya mutu a lamarin yayin da wasu akalla bakwai suka samu raunuka daban-daban.

Nan take aka garzaya da su Asibitin Kwararru da ke Gashua domin jinya, kamar yadda majiyar da ta nemi a sakaya sunanta ta shaida wa manema labarai.

assu news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

IGP ya ba da umarnin bincike kan bidiyon ƙorafin wani tsohon ɗansanda

Babban Sufetan ‘Yan Sandan Najeriya, Kayode Adeolu Egbetokun, ya...

Amurka za ta bayar da gudunmawar dala miliyan 30 ga ‘yan Gaza

Amurka za ta ba da tallafin dala miliyan talatin...

Iran na binciken ɓarnar da aka yi cibiyoyin nukiliyar ƙasar

Ministan harkokin waje na Iran ya amince an yi...

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karo na farko

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karon farko...

Sojoji na zaman makoki na kwanaki 3 bayan an kashe Jami’ai 17

Rundunar Sojin sama ta bayyana fara zaman makoki na...

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da...

Sojoji sun mayar da martani kan ‘Yan ta’addan Neja

Dakarun Sojin Saman kasar nan, sun ce sun ƙaddamar...

Kotu ta yanke wa Matashin da ya kashe Budurwarsa hukuncin kisa

Kotun babban birnin jihar Nasarawa ta yanke wa wannan...

PDP ta yi watsi da matakin shugaban jam’iyyar da ya dauka

Kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP, ya yi watsi da...

Tinubu zai sanya hannu kan sabbin dokokin haraji

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai sanya hannu kan...

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga...

Kungiyoyi 110 suna bukatar mu yi musu rijista – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta tabbatar da samun buƙatu...
X whatsapp