fidelitybank

Bam ɗin da muka jefa abin tashin hankali ne da ba a ƙara buƙatarsa – Sojoji

Date:

Hedikwatar tsaron Najeriya ta bayyana harin jirgi maras matuƙi na baya-bayan nan da aka kai jihar Kaduna wanda ya halaka mutum kusan 100 a matsayin abin tashin hankali da ba a buƙatar faruwarsa.

A sanarwar da Daraktan yaɗa labarai, Manjo Janar Edward Buba ya fitar, an kai harin ne sakamakon bayanan sirrin da aka samu cewa akwai ƴan bindiga a yankin.

Harin dai ya faru ne dai-dai lokacin da mutane a ƙauyen Tudun Biri suke gudanar da taron bikin Mauludi.

Tuni dai gwamnan jihar ta Kaduna, Uba Sani ya ba da umarnin gudanar da bincike mai zurfi kan lamarin da ya jikkata wasu gommai.

Rundunar sojin ƙasar ta ce lokaci zuwa lokaci ta kan ƙaddamar da irin wannan hari kan ƴan bindiga da a wani lokacin yake shafar al’ummar gari.

Zuwa yanzu, waɗanda suka jikkata suna samun kulawa a asibitin gwamnati a jihar.

Jihar Kaduna na fama da matsalar tsaro inda tsawon shekaru, ƴan bindiga ke kai hare-hare tare da yin garkuwa da jama’a don neman kuɗin fansa.

world news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp