fidelitybank

Bajintar ɗaliban Najeriya a gasar Turanci ta nuna ingancin ilimi a ƙasa – Tinubu

Date:

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu, ya taya ƴanmatan nan uku da suka nuna bajinta a wata gasa ta TeenEagle da aka yi a Birtaniya.

Ƴanmatan Nafisa Abdullahi mai shekara 17 ta haskaka a gasar Turanci yayin da Rukayya Muhammad Fema mai shekara 15 ta fi kowa hazaƙa a muhawara da Hadiza Kashim Kalli ta lashe kyautar mafi fiƙira.

Cikin wata sanarwa da kakakin shugaban ƙasar, Bayo Onanuga ya fitar, Tinubu ya yaba wa matasan ƴan Najeriyar saboda bajintar da suka nuna a gasar .

Ya kuma yaba wa makarantu da sauran cibiyoyin karatu inda ya ce irin waɗannan nasarori na bayyana yanayin ingancin da ilimi ke da shi a Najeriya.

Shugaba Tinubu ya bayyana ilimi a matsayin tushen duk wani ci gaban ƙasa, abin da ya sa ma a cewarsa gwamnatinsa ke fifita ɓangaren tare da ganin ta kawar da duk wata matsala ta kuɗi da za ta hana ƴan ƙasar ci gaba da karatu ta hanysar tsarin tallafin karatu na NELFUND.

Shugaban ƙasar ya kuma ƙarfafa wa Nafisa da Rukayya da Hadiza gwiwar mayar da hankali a karatu tare da yi masu fatan samun ƙarin nasarori a rayuwarsu.

vgn news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnan Kano ya kori mataimansa na musamman kan belin Danwawu

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya amince da...

Tsohon Minista a mulkin Buhari ya mutu

Allah ya yi wa tsohon ministan noma da raya...

Kashi 70 na yankin Bukuyum ta Kudu na ƙarƙashin ƴan Bindiga – Ɗan majalisa

Rahotanni daga yakin ƙaramar hukummar Bukuyum na jihar Zamfara...

Goodluck ya fi dacewa ya zama dan takara a 2027 – Lamido

Tsohon Gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido ya ce Tsohon...

An gargadi al’umma su yi taka tsan-tsan da ambaliyar ruwan sama

Yayin da ake ci gaba da fuskantar saukar ruwan...

Gwamnatin Tarayya za ta gina hanyar sufurin jirgin ƙasa a Kano

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta samar da titin...

Abin da ya sa muke ci gaba da tsare Sowore – Ƴansanda

Kwamishinan ƴansanda mai kula da sashen kai ɗauki na...

INEC za ta bai wa ɗaurarru damar kaɗa ƙuri’a a lokacin zaɓuka

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta ta duba yiwuwar bai...

Mai ya jawo Matan Zamfara su ka yi zanga-zanga

Ɗaruruwan mata ne tsofaffi da masu shawarya suka gudanar...

Aƙalla mutane 24,000 ne suka ɓata saboda Boko Haram a Najeriya

Kungiyar Agaji ta Red Cross ta bayyana cewa aƙalla...

‘Yansanda ku gaggauta sakin Sowore – Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP, Peter...

PDP ta gargaɗi mambobinta kan goyon bayan Tinubu

Babbar jam'iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ta gargaɗi...
X whatsapp