fidelitybank

Bai kamata ace shugaban jam’iyyar PDP da ɗan takara sun fito daga Arewa ba – Walid Jibrin

Date:

Shugaban Kwamitin amintattu na babbar jam’iyyar adawa, PDP, Walid Jibrin, ya ce, bai kamata a ce shugaban jam’iyyar PDP da dan takarar shugabancin kasa na jam’iyyar su fito daga arewacin kasar ba.

Walid Jibrin ya bayyana haka ne a wata hira da aka yi da shi a Channels TV.

Jibrin ya ce dan takarar shugaban kasa na PDP Atiku Abubakar da shugaban jam’iyyar na kasa, Iyorchia Ayu, dukkansu daga arewacin kasar suka fito inda ya ce hakan ba daidai ba ne.

Ya ce “A hakikanin gaskiya bai dace a ce da shugaban jam’iyya da dan takarar shugaban kasa na jam’iyya da kuma shugaban kwamitin amintattu na jam’iyya duk su fito daga yanki guda ba. Abin da ya kamata mu yi shi ne mu yi abin da ya dace da muradin jam’iyya ba son rai ba.”

Shugaban kwamitin amintattu na jam’iyyar, wanda ya ce bai damu ya sauka daga mukamin nasa ba don ci gaban jam’iyyar, ya kara da cewa jam’iiyarsu ce za ta samu nasara a zaben shugaban kasa mai zuwa.

Kalaman Walid Jibrin na zuwa ne a yayin da ake ci gaba da rikici a jam’iyyar ta PDP, tun bayan tsayar da Atiku Abubakar a matsayin wanda zai tsaya wa jam’iyyar takarar shugaban kasa.

legit latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp