fidelitybank

Bai kamata a dauki aikin Soja a matsayin sana’ar samun kudi ba – Laftanar Farouk

Date:

Babban hafsan sojin ƙasa, Laftanar Janar Forouk Yahaya, ya ce, bai kamata a ɗauki aikin soja a matsayin sana’ar samun kuɗi ba kamar sauran sana’o’i.

Janar Yahaya ya bayyana haka ne bayan da ya ziyarci sansanin tantance sabbin sojojin da rundunar sojin ƙasar za ta ɗauka aiki a cibiyar tantance lafiya da cancantar soji da ke dajin Falgore a jihar Kano da ke arewacin ƙasar.

Yayin da yake bayyana matsayarsa, babban hafsan sojin ƙasa na ƙasar ya ce saɓanin sauran sana’o’i, shi aikin soji amsa kira ne domin tsaron ƙasa, dan haka ake buƙatar ‘yan ƙasar masu cikakkiyar lafiyar gaɓɓai da ƙwaƙwale tare da fikira.

Ya ƙara da cewa shiga aikin soji ba sana’a ce ta samun kuɗi ba, a maimakon haka aiki ne na hidimta wa ƙasa, dan haka yake buƙatar sadaukarwa, da jajircewa da kuma juriya, domin kuwa ba aiki ne na gama-garin mutane ba.

Babban hafsan sojin ƙasan ya shawarci matasan da ake tantancewar da su maida hankali domin kuwa waɗanda suka nuna ƙwazo ne kaɗai za su samu nasarar tsallake matakin tantancewar.

tribune newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...
X whatsapp