Shugaban kungiyar gwamnonin kuma gwamnan jihar Kebbi, Alhaji Atiku Bagudu, ya bayyana cewa, jamâiyyar APC mai mulki ba za ta sauya ranar babban taron kasa na ranar 26 ga Maris ba, duk da sauya jadawalin da aka yi na babban zaben shekarar 2023.
Ya bayyana haka ne a ranar Talata a lokacin da yake gabatar da tambayoyi daga manema labarai a fadar shugaban kasa bayan ganawarsa da shugaban kasa Muhammadu Buhari a fadar shugaban kasa da ke Abuja.
Jadawalin da Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta fitar a ranar Asabar bayan da shugaban kasar ya rattaba hannu kan dokar gyaran dokar zabe ta 2022 a ranar Jumaâar da ta gabata, ya sanya jamâiyyun siyasa fuskantar matsin lamba kan su cika waâadin da aka sanya na zaben fidda gwani.