Gwamnatin jihar Kano, ta kafa kwamitin da zai rinka kula da karbar ƙudaden shiga daga gidajen da a ke gudanar da taro da na yawon buɗe idanu karkashin shugabancin Baffa Babba Ɗan Agundi.
Gwamnan Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana hakan a fadar gwamnati.
Ya ce, “Mun tattauna da masu irin wadannan gidajen na taruka da masu otal-otal da sauran su, inda su ka bada goyon bayan su kasancewar kudaden za su taimaka wajen dorewar manyan ayyuka a Kano”. Inji Ganduje.
Bayan kammala jawabin gwamna shi ma shugaban kwamitin, Baffa Babba Dan Agundi, ya ce,”Za mu yi aiki yadda ya kamata, saboda ci gaban jihar Kano wajen abin ko yi da ita”.
“Yanzu haka mun tattauna da mutane 570 masu gidajen abinci da otal-otal da wuraren shakatawa, kuma dukannin shugabannin sun nuna goyon bayan su kan wannan sabuwar dokar”. A cewar Baffa.