fidelitybank

Badakalar Kudi: Gwamnan Zamfara da mataimakin sa sun dau zafi

Date:

Gwamnan jihar Zamfara, Bello Matawalle, da mataimakinsa, Barista Mahdi Gusau, sun fara musayar yawu kan karkatar da kuɗaɗen al’ummar jihar da ake zargi.

Daily Trust ta rawaito cewa, Sakataren mataimakin gwamna, Aminu Umar, ya kalubalanci Matawalle ya fito ya yi wa al’umma jawabin yadda ya kashe Naira biliyan 31, waɗan da ya karba a watanni 31.

Umar ya bukaci gwamnan ya yi bayani dalla-dalla kan yadda ya tafiyar da kuɗaɗen da aka ware masa na tsaro, kasafin Ofishinsa, Sakatarensa, da kuma gidan gwamnati tun da ya hau mulki.

Ya ce, tun farkon kafa gwamnati, gwamna na karbar Naira miliyan 600 na tsaro duk wata, miliyan 350 tsabar kuɗin Ofishinsa, Miliyan 30 na ofishin PPS da kuma miliyan 30 na kasafin fadar gwamnati. Wadna kuɗin sun kama Naira Biliyan 1.1 duk wata, wanda idan ka nunka sau 31, kuɗin sun zama Biliyan 31.3.

Sai  dai da yake martani kan maganar, kakakin gwamna Bello Matawalle, Zailani Bappa, ya yi fatali da zargin, inda ya ce, farfaganda ce kawai suke yi, domin  kuwa idan suna da kwakkwarar hujja su rubuta korafi kan mai girma gwamna su gabatar wa hukumomin dake da alhaki. Wannan zancen na su na nuna cewa, kasala ta hana su gano gaskiya. Uban gidansu na daga cikin waɗan da suka tafiyar da harkokin gwamnati na shekaru biyu da rabi, me ya sa ba su bankado lamarin ba tun a baya?.

nigerian 
news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp