Gwamnan jihar Zamfara, Bello Matawalle, da mataimakinsa, Barista Mahdi Gusau, sun fara musayar yawu kan karkatar da kuɗaɗen al’ummar jihar da ake zargi.
Daily Trust ta rawaito cewa, Sakataren mataimakin gwamna, Aminu Umar, ya kalubalanci Matawalle ya fito ya yi wa al’umma jawabin yadda ya kashe Naira biliyan 31, waɗan da ya karba a watanni 31.
Umar ya bukaci gwamnan ya yi bayani dalla-dalla kan yadda ya tafiyar da kuɗaɗen da aka ware masa na tsaro, kasafin Ofishinsa, Sakatarensa, da kuma gidan gwamnati tun da ya hau mulki.
Ya ce, tun farkon kafa gwamnati, gwamna na karbar Naira miliyan 600 na tsaro duk wata, miliyan 350 tsabar kuɗin Ofishinsa, Miliyan 30 na ofishin PPS da kuma miliyan 30 na kasafin fadar gwamnati. Wadna kuɗin sun kama Naira Biliyan 1.1 duk wata, wanda idan ka nunka sau 31, kuɗin sun zama Biliyan 31.3.
Sai dai da yake martani kan maganar, kakakin gwamna Bello Matawalle, Zailani Bappa, ya yi fatali da zargin, inda ya ce, farfaganda ce kawai suke yi, domin kuwa idan suna da kwakkwarar hujja su rubuta korafi kan mai girma gwamna su gabatar wa hukumomin dake da alhaki. Wannan zancen na su na nuna cewa, kasala ta hana su gano gaskiya. Uban gidansu na daga cikin waɗan da suka tafiyar da harkokin gwamnati na shekaru biyu da rabi, me ya sa ba su bankado lamarin ba tun a baya?.