Rundunar ‘yan sandan babban birnin Tarayyar Abuja ta sanar da dokar hana zirga-zirga tsakanin mazauna garin daga karfe 8 na safe zuwa 3 na yamma, yayin gudanar da zabukan kananan hukumomin birnin a yau Asabar 12 ga watan Fabirariru.
Shugaban ‘yan sandan birnin Babaji Sunday, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma’a.
Kamfanin dillancin labarai na NAN, ya rawaito cewa, a ranar Alhamis rundunar ta sanar da cewa, hana zirga-zirgar zai fara aiki ne daga 12 daren ranar Juma’a zuwa karfe 4 ranar Asabar.
Sai dai a safiyar juma’a rundunar ta sanar da cewa, ta sassauta matakin kwana daya gabanin zaben, inda suka bai wa mutane shawarar ci gaba da al’amuransu na yau da kullum.