fidelitybank

Babu wata hamayya da ta rage a Najeriya – Bafarawa

Date:

Tsohon gwamnan jihar Sokoto, Alhaji Attahiru Dalhatu Bafarawa , ya ce a yanzu babu wata hamayya da ta rage a fagen siyasar Najeriya.

A tattaunawarsa da BBC ya ce ‘yan siyasar kasar su ne ke hamayya da kansu da cutar juna game da neman mukamai ba tare da sun anfana wa talakawa wani abu ba.

Bafarawa ya bayyana hakan ne ganin yadda wasu jiga-jigan jam’iyyun hamayya na kasar ke tururuwa suna komawa jam’iyya mai mulki ta APC a wannan tsakanin yayin da ya rage wajen shekara biyu a yi babban zabe na gaba, a 2027.

Tsohon gwamnan ya yi zargin cewa duk wannan sauya sheka da ‘yansiyasar na bangaren hamayya ke yi suna tafiya jam’iyya mai mulki ba don komai suke yi ba na amfanin talaka, face don kansu suke yi, saboda haka ya ce siyasar hamayya ta mace a kasar a yanzu – babu akida.

”Saboda haka cikin duhu ake da mai nema da wanda ake nema, shi mai nema idonshi sun rufe ba imani ba tausayi shi dai ya samu mukami, shi kuma talaka idonshi sun rufe ga yunwa ga talauci ga jahilci saboda haka duk a yamutse ake,” in ji shi.

Alhaji Attahiru ya ce, ”adawa da ake adawa kowa kanshi yake adawa, me zai samu in ya ga waccan kofar ta rufe bai jin kunya bai jin tsoro hanyar nan da ya bata, ya bace ta nan zai sake daowa.”

”Ba wata adawa da ake yanzu kowa adawar da yake yi me zai samu, da zarar ya samu babu adawa shi talaka sai dai ya yi ta kanshi,” ya ce.

Ya kara da cewa abin takaici za ka ga ‘yansiyasar ana ta fada da juna amma ba don talaka suke yi ba sai dai don mukami, kuma mukamin da suke fadan a kai sun taba rike shi amma me suka yi da suka rike da a yanzu suke fada don su sake samunshi?

”Yanzu da kake son sake rike mukamin me ka yi wanda ba ka yi a baya ba, wanda zai sa Arewa ta ci gaba?”

Dansiyasar ya ce yankin Arewa yana cikin wani mawuyacin hali na koma-baya.

Ya ce duk inda ka ci mutum da yakin ilimi ka jefa masa jahilci to ka gama da shi.

”Yanzu mu nan dama-dama gare mu yaranmu kashi 70 cikin dari wallahi ba su da ilimi. To ta yaya kasa ko yanki za su ci gaba ba ilimi?” Ya ce.

Ya kara da cewa, ”sai ka ga shin su talakawan ga da ake wa magana sun san ciwon kansu koko mene ne?”

”Sa’annan su ‘yansiyasar da ke son su ja talakawa da gaske suke yi tsakani da Allah Suke yi?”

bbc news 
nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp