Sakatare-janar na ƙungiyar ƙasashe masu arzikin man fetur, OPEC, ya shaida wa BBC cewa babu wata alama ta faɗuwar farashin man a nan kusa.
Haitham Al Ghais ya ce shawarar da mambobin ƙungiyar suka yanke ta rage man da suke samarwa har zuwa karshen shekara mai zuwa na iya haifar da ƙarancinsa.
Manazarta sun ce hakan na iya sa farashin ya haura dala ɗari kan ganga ɗaya.
Mista Ghais ya yi gargaɗin cewa za a fuskanci mummunan sakamako idan ɓangaren makamashi ya daina saka hannun jari a harkar mai, wanda ya ce zai iya haifar da taɓarɓarewar kasuwar man, da kuma haifar da ƙarancinsa.
Sai dai Hukumar Kula da Makamashi ta Duniya ta yi gargaɗin cewa dole ne a ɗauki ƙwakkwaran mataki kan hanyoyin samar da man, matsawar ana son kaucewa tasirin sauyin yanayi.