fidelitybank

Babu wasu ‘yan Najeriya da suka bata a hukumance – Sadiya

Date:

Ministar Ma’aikatar jinkai da agajin gaggawa ta kasa, Sadiya Umar-Farouk, ta ce babu wani takamaiman adadi mutanen da suka ɓata a Najeriya a hukumance, balle a dogara da shi a yi rijista.

Ta bayyana haka ne a Abuja ranar Talata a wani taron masu ruwa da tsaki wanda ma’aikatarta da hadin gwiwar Hukumar Red Cross suka shirta da kuma hukumar kare haƙƙin ɗan adam.

Sadiya wadda babban sakataren ma’aikatar Dr Nasiru Sani Gwarzo ya wakilta ya ce, a halin da ake ciki yanzu Najeriya ba ta tsari a hukumance domin tunkarar matsalar mutanen da suke ɓata a ƙasar.

Ta ce gwamnatin tarayya “ta damu kan yadda mutane ke wasa da taruwarsu saboda tafiye-tafiye”.

Tace tafiyar ciranin da ‘yan Najeriya ke yi, wadda ke haɗawa har da ƙananan yara domin tsallaka iyakokin kasar, ta sahara da tekun maliya domin samun rayuwa mai kyau a kowacce shekara, tana taimakawa wajen ɓacewar mutane.

Ta ƙara da cewa:”ƙididdigar da aka fitar da kwanan nan ta nuna cikin mutum 64,000 da suka ɓata a a nahiyar Afrika, 25,000 ‘yan Najeriya ne, kuma sama da 14,000 yara ne daga ciki.”

Shugaban ICRC a Najeriya Yann Bonzon, ya ce a kalla iyalai 13,000 a Najeriya na neman ‘yan uwansu da suka ɓata.

legitnews.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp