Ministar Ma’aikatar jinkai da agajin gaggawa ta kasa, Sadiya Umar-Farouk, ta ce babu wani takamaiman adadi mutanen da suka ɓata a Najeriya a hukumance, balle a dogara da shi a yi rijista.
Ta bayyana haka ne a Abuja ranar Talata a wani taron masu ruwa da tsaki wanda ma’aikatarta da hadin gwiwar Hukumar Red Cross suka shirta da kuma hukumar kare haƙƙin ɗan adam.
Sadiya wadda babban sakataren ma’aikatar Dr Nasiru Sani Gwarzo ya wakilta ya ce, a halin da ake ciki yanzu Najeriya ba ta tsari a hukumance domin tunkarar matsalar mutanen da suke ɓata a ƙasar.
Ta ce gwamnatin tarayya “ta damu kan yadda mutane ke wasa da taruwarsu saboda tafiye-tafiye”.
Tace tafiyar ciranin da ‘yan Najeriya ke yi, wadda ke haɗawa har da ƙananan yara domin tsallaka iyakokin kasar, ta sahara da tekun maliya domin samun rayuwa mai kyau a kowacce shekara, tana taimakawa wajen ɓacewar mutane.
Ta ƙara da cewa:”ƙididdigar da aka fitar da kwanan nan ta nuna cikin mutum 64,000 da suka ɓata a a nahiyar Afrika, 25,000 ‘yan Najeriya ne, kuma sama da 14,000 yara ne daga ciki.”
Shugaban ICRC a Najeriya Yann Bonzon, ya ce a kalla iyalai 13,000 a Najeriya na neman ‘yan uwansu da suka ɓata.