fidelitybank

Babu wasu ‘yan Najeriya da suka bata a hukumance – Sadiya

Date:

Ministar Ma’aikatar jinkai da agajin gaggawa ta kasa, Sadiya Umar-Farouk, ta ce babu wani takamaiman adadi mutanen da suka ɓata a Najeriya a hukumance, balle a dogara da shi a yi rijista.

Ta bayyana haka ne a Abuja ranar Talata a wani taron masu ruwa da tsaki wanda ma’aikatarta da hadin gwiwar Hukumar Red Cross suka shirta da kuma hukumar kare haƙƙin ɗan adam.

Sadiya wadda babban sakataren ma’aikatar Dr Nasiru Sani Gwarzo ya wakilta ya ce, a halin da ake ciki yanzu Najeriya ba ta tsari a hukumance domin tunkarar matsalar mutanen da suke ɓata a ƙasar.

Ta ce gwamnatin tarayya “ta damu kan yadda mutane ke wasa da taruwarsu saboda tafiye-tafiye”.

Tace tafiyar ciranin da ‘yan Najeriya ke yi, wadda ke haɗawa har da ƙananan yara domin tsallaka iyakokin kasar, ta sahara da tekun maliya domin samun rayuwa mai kyau a kowacce shekara, tana taimakawa wajen ɓacewar mutane.

Ta ƙara da cewa:”ƙididdigar da aka fitar da kwanan nan ta nuna cikin mutum 64,000 da suka ɓata a a nahiyar Afrika, 25,000 ‘yan Najeriya ne, kuma sama da 14,000 yara ne daga ciki.”

Shugaban ICRC a Najeriya Yann Bonzon, ya ce a kalla iyalai 13,000 a Najeriya na neman ‘yan uwansu da suka ɓata.

breaking news in nigeria today 2021

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An gargadi al’umma su yi taka tsan-tsan da ambaliyar ruwan sama

Yayin da ake ci gaba da fuskantar saukar ruwan...

Gwamnatin Tarayya za ta gina hanyar sufurin jirgin ƙasa a Kano

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta samar da titin...

Abin da ya sa muke ci gaba da tsare Sowore – Ƴansanda

Kwamishinan ƴansanda mai kula da sashen kai ɗauki na...

INEC za ta bai wa ɗaurarru damar kaɗa ƙuri’a a lokacin zaɓuka

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta ta duba yiwuwar bai...

Mai ya jawo Matan Zamfara su ka yi zanga-zanga

Ɗaruruwan mata ne tsofaffi da masu shawarya suka gudanar...

Aƙalla mutane 24,000 ne suka ɓata saboda Boko Haram a Najeriya

Kungiyar Agaji ta Red Cross ta bayyana cewa aƙalla...

‘Yansanda ku gaggauta sakin Sowore – Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP, Peter...

PDP ta gargaɗi mambobinta kan goyon bayan Tinubu

Babbar jam'iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ta gargaɗi...

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...
X whatsapp