Jam’iyyar Labour Party, ta musanta labarin da ake ta yadawa cewa shugabanta na kasa Barrister Julius Abure ya sauka, sannan kuma ya yi watsi da dan takararta na shugaban kasa Peter Obi.
A wani sakon Twitter da jam’iyyar ta sanya ta ce abokan hamayya ne suke yada labarin cewa shugaban ya ajiye mukamin.
A jiya Laraba ne wasu kafafe suka rika yada labarin cewa shugaban ya ajiye mukamin sannan kuma ya yi watsi da Mista Peter Obi wanda shi ne dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar.
Jam’iyyar kamar sauran takwarorinta ta shiga yakin neman zabe na dan takarar tata a fadin kasar, domin tunkarar zaben na ranar 25 ga watan Fabrairu 2023.
Za a yi zaben na shugaban kasa da ‘yan majalisun dokoki na tarayya a wannan rana ta 25 ga wata.
Yayin da za a yi zaben gwamnonin jihohi da kuma ‘yan majalisun dokoki na jiha ranar 11 ga watan Maris na 2023.